fidelitybank

An kama mutane biyar da zargin tsafi a Ogun

Date:

An kama wasu mutane biyar da ake zargi da aikata ayyukan tsafi a Ososa da ke karamar hukumar Odogbolu a jihar Ogun.

An kama wadanda ake zargin ne biyo bayan samun bayanan da ‘yan sanda suka samu a hedikwatar sashin Odogbolu.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Abimbola Oyeyemi, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar.

Karanta Wannan: Idan aka cigaba da kama mutanen mu zamu mamaye ofishin ‘yan sanda – PDP

Ya ce ’yan kungiyar da ke da alhakin tono gawarwaki a cikin al’ummar Ososa, sun shirya wani wuri a cikin garin domin sake yin wani zagaye na girbin sassan jikin dan Adam.

Da yake bayyana wadanda ake zargin Oshole Fayemi, Osemi Adesanya, Ismaila Seidu, Oseni Oluwasegun da Lawal Olaiya, kakakin rundunar ‘yan sandan ya zarge su da tono gawarwaki daga cikin kaburburansu tare da cire wasu sassan jikinsu domin yin ibada.

Oyeyemi ya kara da cewa a cikin sanarwar, wadanda ake zargin suna da shekaru daga 30 zuwa 60.

“Bayan samun labarin, DPO Odogbolu, CSP Godwin Idehai, ya tattara mutanensa tare da kutsawa maboyar wadanda ake zargin inda aka kama biyar daga cikinsu,” inji shi.

“A yayin da ake yi musu tambayoyi, wadanda ake zargin sun yi ikirari cewa a zahiri suna sana’ar tono gawarwaki ne daga kaburburansu kuma suna sayar da sassan gawar ga masu sayan su da ke bukatar ta domin neman kudi.”

Da yake mayar da martani kan kamun, kwamishinan ‘yan sandan jihar Ogun, Frank Mba, ya bayar da umarnin a mika wadanda ake zargin zuwa sashin binciken manyan laifuka na jihar domin gudanar da bincike mai zurfi tare da gurfanar da su gaban kuliya.

latest legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp