An kama wasu mutane biyar da ake zargi da aikata ayyukan tsafi a Ososa da ke karamar hukumar Odogbolu a jihar Ogun.
An kama wadanda ake zargin ne biyo bayan samun bayanan da ‘yan sanda suka samu a hedikwatar sashin Odogbolu.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Abimbola Oyeyemi, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar.
Karanta Wannan: Idan aka cigaba da kama mutanen mu zamu mamaye ofishin ‘yan sanda – PDP
Ya ce ’yan kungiyar da ke da alhakin tono gawarwaki a cikin al’ummar Ososa, sun shirya wani wuri a cikin garin domin sake yin wani zagaye na girbin sassan jikin dan Adam.
Da yake bayyana wadanda ake zargin Oshole Fayemi, Osemi Adesanya, Ismaila Seidu, Oseni Oluwasegun da Lawal Olaiya, kakakin rundunar ‘yan sandan ya zarge su da tono gawarwaki daga cikin kaburburansu tare da cire wasu sassan jikinsu domin yin ibada.
Oyeyemi ya kara da cewa a cikin sanarwar, wadanda ake zargin suna da shekaru daga 30 zuwa 60.
“Bayan samun labarin, DPO Odogbolu, CSP Godwin Idehai, ya tattara mutanensa tare da kutsawa maboyar wadanda ake zargin inda aka kama biyar daga cikinsu,” inji shi.
“A yayin da ake yi musu tambayoyi, wadanda ake zargin sun yi ikirari cewa a zahiri suna sana’ar tono gawarwaki ne daga kaburburansu kuma suna sayar da sassan gawar ga masu sayan su da ke bukatar ta domin neman kudi.”
Da yake mayar da martani kan kamun, kwamishinan ‘yan sandan jihar Ogun, Frank Mba, ya bayar da umarnin a mika wadanda ake zargin zuwa sashin binciken manyan laifuka na jihar domin gudanar da bincike mai zurfi tare da gurfanar da su gaban kuliya.