Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce, ta kama wasu mutane takwas da ake zargi da hannu a kisan jami’anta a wani bincike na gaskiya a yankin Ughelli na jihar Delta.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar, ACP Olumuyiwa Adejobi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar a Abuja.
Ya ce a ranar 23 ga watan Fabarairu ne jami’an da ke aikin gano gaskiya aka yi musu kwanton bauna yayin da wasu da ke aikin ceto su ma aka yi musu kwanton bauna, wanda ya yi sanadin mutuwar ‘yan sanda shida.
Adejobi ya ce kamen ya biyo bayan wani gagarumin bincike da jami’an ‘yan sandan suka yi.
A cewarsa, an fara cafke mutane biyar da ake zargi jim kadan bayan faruwar lamarin yayin da aka kama wasu karin uku a wurare daban-daban.
Ya ce kama karin ukun ya biyo bayan kalamai ne da hadin kan wadanda aka kama da farko.
Adejobi ya ce a halin yanzu wadanda ake zargin suna hannun ‘yan sanda, inda suke taimakawa wajen gudanar da bincike.
Ya ce rundunar ‘yan sandan Najeriya ta dukufa wajen ganin an kama duk wadanda ke da hannu wajen aikata kisan kai da sauran laifuka makamantansu tare da gurfanar da su gaban kuliya cikin gaggawa.
Kakakin ‘yan sandan ya ce nan ba da jimawa ba za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu, tare da kwararan hujjoji, da zarar an kammala bincike.
Ya ce rundunar ‘yan sandan ta yi matukar bakin ciki da wannan danyen aikin na cin zarafin da aka yi wa jami’anta da ke gudanar da ayyukansu na kare da yi wa al’umma hidima.
“Tunaninmu da addu’o’inmu suna tare da iyalan jami’an da suka mutu a wannan mawuyacin lokaci.
“Muna so mu sake jaddada cewa wadanda suka kashe jami’an mu a cikin wannan halin da ake ciki da kuma wasu da yawa, sun kashe zaman lafiya kuma babu daya daga cikinsu da zai tafi ba tare da hukunci ba,” in ji shi.
Idan dai za a iya tunawa, an kashe jami’an da ke bakin aiki a yankin Ughelli na jihar a ranar 23 da 26 ga watan Fabrairu, yayin da wasu shida suka bace.