fidelitybank

An kama mutane 8 da zargin kashe jami’in ‘yan sanda a Delta

Date:

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce, ta kama wasu mutane takwas da ake zargi da hannu a kisan jami’anta a wani bincike na gaskiya a yankin Ughelli na jihar Delta.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar, ACP Olumuyiwa Adejobi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar a Abuja.

Ya ce a ranar 23 ga watan Fabarairu ne jami’an da ke aikin gano gaskiya aka yi musu kwanton bauna yayin da wasu da ke aikin ceto su ma aka yi musu kwanton bauna, wanda ya yi sanadin mutuwar ‘yan sanda shida.

Adejobi ya ce kamen ya biyo bayan wani gagarumin bincike da jami’an ‘yan sandan suka yi.

A cewarsa, an fara cafke mutane biyar da ake zargi jim kadan bayan faruwar lamarin yayin da aka kama wasu karin uku a wurare daban-daban.

Ya ce kama karin ukun ya biyo bayan kalamai ne da hadin kan wadanda aka kama da farko.

Adejobi ya ce a halin yanzu wadanda ake zargin suna hannun ‘yan sanda, inda suke taimakawa wajen gudanar da bincike.

Ya ce rundunar ‘yan sandan Najeriya ta dukufa wajen ganin an kama duk wadanda ke da hannu wajen aikata kisan kai da sauran laifuka makamantansu tare da gurfanar da su gaban kuliya cikin gaggawa.

Kakakin ‘yan sandan ya ce nan ba da jimawa ba za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu, tare da kwararan hujjoji, da zarar an kammala bincike.

Ya ce rundunar ‘yan sandan ta yi matukar bakin ciki da wannan danyen aikin na cin zarafin da aka yi wa jami’anta da ke gudanar da ayyukansu na kare da yi wa al’umma hidima.

“Tunaninmu da addu’o’inmu suna tare da iyalan jami’an da suka mutu a wannan mawuyacin lokaci.

“Muna so mu sake jaddada cewa wadanda suka kashe jami’an mu a cikin wannan halin da ake ciki da kuma wasu da yawa, sun kashe zaman lafiya kuma babu daya daga cikinsu da zai tafi ba tare da hukunci ba,” in ji shi.

Idan dai za a iya tunawa, an kashe jami’an da ke bakin aiki a yankin Ughelli na jihar a ranar 23 da 26 ga watan Fabrairu, yayin da wasu shida suka bace.

thisday news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp