fidelitybank

An kama mutane 8 da suka yi garkuwa da dalibai a jihar Ekiti

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Ekiti ta ce, ta kama mutum takwas da suka yi garkuwa da wasu ɗalibai da malaman makarantar Apostolic Faith a Emure-Ekiti, da ke jihar.

Kwamishinan ‘yansandan jihar CP Adeniran Akinwale, ne ya bayyana haka lokacin da yake holen masu garkuwar a shalkwatar rundunar da ke birnin Ado-Ekiti, ranar Juma’a.

Mista Akinwale ya ce an kashe ɗaya daga cikin masu garkuwar a lokacin musayar wuta da jami’an ‘yansanda.

Kwamishinan ya ƙara da cewa maharan su ne kuma suka yi garkuwa da shugaban jam’iyyar APC na jihar, Hon. Paul Omotoso a shekara 2023

”Binciken farko ya nuna cewa Sumo Karami, tare da yaransa ne suka sace tare da yin garkuwa da ɗaliban nan da malamansu a Emre-Ekiti ranar 29 ga watan Janairu”, in ji kwamishinan.

Ya ƙara da cewa “Mun gano wayar da masu garkuwar suka yi amfani da ita wajen kira domin neman kuɗin fansa don sakin ɗaliban da malaman a hannun maharan”.

“Haka kuma an gano wasu abubuwa tare da maharan, daga ciki har da bindiga ƙirar AK-47 da wata ƙaramar bindiga da harsasai biyar a cikinta, sannan kuma da abun kurtun AK-47 21 maƙare da harsasan, sa sauran abubuwa”, in ji mista Akinwale.

kano news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp