Jami’an tsaron Ethiopia sun ce sun sun tsare mutum 76 bisa zargin tayar da tarzoma ranar Litinin yayin da Musulmai suka taru domin gudanar da sallar Idi a Addis Ababa, babban birnin kasar.
‘Yan sanda sun yi amfani da barkonon-tsohuwa wajen tarwatsa taron jama’a lokacin da lamarin ya faru ko da yake babu rahoton rasa rai.
Dubban mutane ne suke halartar sallar Idi da aka gudanar a babban filin wasan kasar yayin da tarzomar ta barke. A cewar BBC.
Lamarin ya faru ne kwanaki kadan bayan da aka tayar da jijiyoyin wuya tsakanin Musulmai da Kiristoci a sassan kasar bayan an kashe Musulmai 20 da ke halartar jana’iza a makon jiya a arewacin Ethiopia.
Bayan aukuwar lamarin a birnin Gondar, an gudanar da jerin zanga-zanga a wurare da dama da kuma tarzoma ciki har da kona akalla coci uku a kudancin kasar.