fidelitybank

An kama mutane 76 da suka hana musulman Habasha yin sallar Idi

Date:

Jami’an tsaron Ethiopia sun ce sun sun tsare mutum 76 bisa zargin tayar da tarzoma ranar Litinin yayin da Musulmai suka taru domin gudanar da sallar Idi a Addis Ababa, babban birnin kasar.

‘Yan sanda sun yi amfani da barkonon-tsohuwa wajen tarwatsa taron jama’a lokacin da lamarin ya faru ko da yake babu rahoton rasa rai.

Dubban mutane ne suke halartar sallar Idi da aka gudanar a babban filin wasan kasar yayin da tarzomar ta barke. A cewar BBC.

Lamarin ya faru ne kwanaki kadan bayan da aka tayar da jijiyoyin wuya tsakanin Musulmai da Kiristoci a sassan kasar bayan an kashe Musulmai 20 da ke halartar jana’iza a makon jiya a arewacin Ethiopia.

Bayan aukuwar lamarin a birnin Gondar, an gudanar da jerin zanga-zanga a wurare da dama da kuma tarzoma ciki har da kona akalla coci uku a kudancin kasar.

vanguardnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin É—an kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...
X whatsapp