fidelitybank

An kama mutane 5 da zargin satar man Dizal

Date:

An kama wasu mutane 5 yayin da suke satar Man Fetur da ake kira Automotive Gas Oil, wanda aka fi sani da Diesel a jihar Ogun.

DAILY POST ta samu cewa wasu jami’an So-Safe Corps reshen jihar Ogun ne suka kama wadanda ake zargin suna aikata laifin a wani kamfanin gine-gine da ke Siun a karamar hukumar Obafemi/Owode a jihar.

Kakakin rundunar So-Safe Corps, Moruf Yusuf, ya ce jami’an rundunar da ke hedikwatar sashin Owode (Egba) ne suka cafke mutanen biyar da misalin karfe 8:30 na yammacin ranar Laraba, 20 ga watan Satumba.

Yusuf ya bayyana sunayen wadanda ake zargin da Abdullah Mohamed (34), Lambo Lack (54), Joel Dawab (40), Wellplus Masua (54), da Seidu Ibrahim (20).

ā€œAn kama wadanda ake zargin ne a wurin da aka aikata laifin, saboda suna satar Automotive Gas Oil (Diesel) na kamfanin gine-ginen hanya (an sakaya sunansa), kafin shiga tsakanin jami’an So-Safe Corps da ke kare kamfanin.ā€ Yace.

Kakakin ya kara da cewa an kwato kwali takwas da kowannen su ya kunshi lita 30 na dizal din da aka sace daga hannun wadanda ake zargin.

An mika wadanda ake zargin da abubuwan baje kolin da aka samu tare da su ga ā€˜yan sanda da ke Owode Egba.

vanguard news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ʙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban ʘsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...

Iran ta zartar da hukuncin kisa a kan Mutane 3

Hukumomi a Iran sun zartar wa mutum uku hukuncin...

Ƴansanda sun kama ʙasurgumin ɗanbindiga a Kaduna

Rundunar ʓansandan jihar Kaduna ta ce, jami'an ta sun...

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...

Rasha tarnaki ce a wajen Tarayyar Turai – Jamus

Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya shaidawa BBC cewa...

Amurka ba ta goyon bayan Isra’ila a harin Syria – Trump

Amurka ta ce ba ta goyon bayan hare-haren da...

Tinubu zai zo Kano ta’aziyyar Dantata

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu zai kai ziyara Kano yau...
X whatsapp