fidelitybank

An kama mutane 5 da zargin satar man Dizal

Date:

An kama wasu mutane 5 yayin da suke satar Man Fetur da ake kira Automotive Gas Oil, wanda aka fi sani da Diesel a jihar Ogun.

DAILY POST ta samu cewa wasu jami’an So-Safe Corps reshen jihar Ogun ne suka kama wadanda ake zargin suna aikata laifin a wani kamfanin gine-gine da ke Siun a karamar hukumar Obafemi/Owode a jihar.

Kakakin rundunar So-Safe Corps, Moruf Yusuf, ya ce jami’an rundunar da ke hedikwatar sashin Owode (Egba) ne suka cafke mutanen biyar da misalin karfe 8:30 na yammacin ranar Laraba, 20 ga watan Satumba.

Yusuf ya bayyana sunayen wadanda ake zargin da Abdullah Mohamed (34), Lambo Lack (54), Joel Dawab (40), Wellplus Masua (54), da Seidu Ibrahim (20).

ā€œAn kama wadanda ake zargin ne a wurin da aka aikata laifin, saboda suna satar Automotive Gas Oil (Diesel) na kamfanin gine-ginen hanya (an sakaya sunansa), kafin shiga tsakanin jami’an So-Safe Corps da ke kare kamfanin.ā€ Yace.

Kakakin ya kara da cewa an kwato kwali takwas da kowannen su ya kunshi lita 30 na dizal din da aka sace daga hannun wadanda ake zargin.

An mika wadanda ake zargin da abubuwan baje kolin da aka samu tare da su ga ā€˜yan sanda da ke Owode Egba.

vanguard (nigeria)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ę“ansandan jihar Kaduna, sun buʙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ʙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ā€˜Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ʙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ā€˜yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp