Gwamnatin tarayya ta ce, ta kama mutum 327 da ake zargi da aikin haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba a faɗin ƙasar nan.
Ministan Ma’adanai Dele Alake ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai a bikin cika shekara ɗaya da kafa rundunar kula da harkokin haƙar ma’adanai ta Mining Marshals (MM).
Kamfanin dillancin labarai na NAN ya ruwaito shi yana cewa, an kama mutanen ne tun daga kafa rundunar a 2024, inda ma’aikatarsa ta yi nasarar gurfanar da 143 daga cikinsu a gaban kotu.
Ya ƙara da cewa babban abin da suka saka a gaba a 2025 shi ne gurfanar da sauran mutanen a gaban shari’a.
An ƙaddamar da rundunar MM ne ranar 21 ga watan Maris na 2024, inda ta fara aiki da dakaru 2,220 kafin su ƙaru zuwa 2,670, a cewar NAN.