fidelitybank

An kama mutane 307 a Abuja

Date:

Rundunar yan sanda a Abuja, ta ce, ta kai samame wata matattarar miyagu inda ta kama mutum dari uku da bakwai da ake zargi da aikata laifuka.

Kwamishinan yan sanda a Abuja, CP Benneth C. Igwe ne ya jagoranci tawagar rundunar ‘Operation Velvet’ wajen kai samame kan matattarar da ke Gidan Dambe a yankin Dei-Dei zuwa Zuba.

Yayin binciken, an gano bindiga daya da alburusai goma sha biyar a hannun wani da yake ikirarin shi jami’in hukumar tsaro ta farin kaya ne.

A cewar sanarwar da kakakin rundunar, SP Josephine Adeh ta wallafa a shafin X, sauran kayayyakin da aka gano sun hada da babura da kunshin tabar wiwi da haramtattun kwayoyi da ake zargi mutanen sun sace ne daga hannun mutanen da ba su ji ba su gani ba.

Kwamishinan yan sandan ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike kan mutanen da aka kama.

A makon da ya gabata ne aka kaddamar da rundunar ta musamman domin kawo karshen duk wasu miyagun laifuka a Abuja.

Kwamishinan ya kuma gargadi yan sanda kan tatsar jama’ar sannan su nuna kwarewa wajen aiwatar da ayyukansu.

legit nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp