Al’amura sun fara lafawa a karamar hukumar Sagamu na jihar Ogun bayan wani zanga-zanga da ya karaɗe garin da safiyar ranar Litinin kan ƙarancin man fetur da kuma sabbin kuɗi.
An far wa bankuna da wuraren kasuwanci tare da cinna musu wuta da lalata motoci, inda aka tilasta wa masu shaguna rufewa.
A cewar kwamishinan ‘yan sandan jihar, Frank Mba, wanda ya jagoranci jami’ansa da kuma sojoji zuwa wurin da lamarin ya faru, ya ce an kama mutum 30 waɗanda ake zargi da hannu a tayar da hankali.
Mazauna garin sun ce an soma tarzomar ne da mislai karfe 5:30 na safe lokacin da akasarin mutane na barci.
Hanyoyi da lamarin ya shafi ya haɗa da titin Oba Erinwole, inda aka far wa rassan bankuna kusan bakwai da kuma lalata na’urorin cirar kuɗi na ATM, abu kuma da ya kassara illahirin garin.
Karanta Wannan: An kama matasa a Delta da suka yi wa Banki rotse
Gidan talabijin na Channels, ya ruwaito cewa wasu ɓata gari sun fasa ginin wani banki, inda suka yi yunkurin shiga ciki domin aikata ta’asarsu.
Sai dai tawagar kwamishinan ‘yan sandan jihar ne tare da haɗin gwiwar sojojin Najeriya suka taka musu burki da kuma takaita yaɗuwar zanga-zangar zuwa wasu wurare a jihar.