fidelitybank

An kama mutane 30 a rikicin kona bankunan Ugun

Date:

Al’amura sun fara lafawa a karamar hukumar Sagamu na jihar Ogun bayan wani zanga-zanga da ya karaɗe garin da safiyar ranar Litinin kan ƙarancin man fetur da kuma sabbin kuɗi.

An far wa bankuna da wuraren kasuwanci tare da cinna musu wuta da lalata motoci, inda aka tilasta wa masu shaguna rufewa.

A cewar kwamishinan ‘yan sandan jihar, Frank Mba, wanda ya jagoranci jami’ansa da kuma sojoji zuwa wurin da lamarin ya faru, ya ce an kama mutum 30 waɗanda ake zargi da hannu a tayar da hankali.

Mazauna garin sun ce an soma tarzomar ne da mislai karfe 5:30 na safe lokacin da akasarin mutane na barci.

Hanyoyi da lamarin ya shafi ya haɗa da titin Oba Erinwole, inda aka far wa rassan bankuna kusan bakwai da kuma lalata na’urorin cirar kuɗi na ATM, abu kuma da ya kassara illahirin garin.

Karanta Wannan: An kama matasa a Delta da suka yi wa Banki rotse

Gidan talabijin na Channels, ya ruwaito cewa wasu ɓata gari sun fasa ginin wani banki, inda suka yi yunkurin shiga ciki domin aikata ta’asarsu.

Sai dai tawagar kwamishinan ‘yan sandan jihar ne tare da haɗin gwiwar sojojin Najeriya suka taka musu burki da kuma takaita yaɗuwar zanga-zangar zuwa wasu wurare a jihar.

vgn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp