fidelitybank

An kama mutane 3 da yi wa mata fyade a Jigawa

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta kama wasu bata gari guda uku bisa zarginsu da fashi da barkonon tsohuwa tare da yi wa wata mata fyade fyade a karamar hukumar Ringim.

Kakakin rundunar DSP. Lawan Shiisu Adam ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai.

Ya ce lamarin ya faru ne a ranar Lahadi da misalin karfe 0200 na safe a kauyen Chori dake karamar hukumar Ringim inda wasu da ba a san ko su wanene ba, dauke da layukan yanka, suka kutsa cikin wani gida, suka afkawa mijin buhunan barkono guda biyar, daga bisani daya daga cikin ‘yan fashin ya yiwa matarsa fyade.

Ya ce bayan samun rahoton, jami’an tsaro na Ringim Dibision sun kai farmaki inda wani Abubakar Isah mai shekaru 25; Umar Ibrahim, mai shekaru 25; da Umar Nasara, mai shekaru 30, dukkansu mazauna kauyen Chori, Ringim LGA, an kama su da laifin aikata laifin.

DSP. Shiisu ya ce da ake yi musu tambayoyi, wadanda ake zargin sun amsa laifin da suka aikata kuma nan take aka mika su zuwa SCID Dutse domin gudanar da bincike mai zurfi.

Ya ce za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu bayan bincike.

nigerianewspapers.com.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp