Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa ta kama mutane 208 da ake zargi tun farkon watan Janairu.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Sikiru Akande wanda ya bayyana hakan a ranar Alhamis, ya kara da cewa daga cikin adadin, an gurfanar da mutum 108 a gaban kotu.
Kwamishinan ya bayyana hakan ne a lokacin da yake gabatar da wadanda ake zargin a hedikwatar ‘yan sandan jihar da ke Yola, inda ya ce an kama wadanda ake zargin ne da laifin yin garkuwa da mutane da fashi da makami da kuma satar shanu.
Ya ce an kama mutanen ne bisa umarnin babban sufeton ‘yan sanda na cewa ya kamata tsarin ‘yan sanda su kara inganta aikin sintiri da dabarun kawar da abubuwan da ba a so a wani bangare na shirye-shiryen babban zaben da za a fara a wata mai zuwa.
“A farkon wannan shekarar, rundunar ta sake sabunta alkawarinta tare da tsara tsarin tsaro don aiwatar da aikin Sufeto Janar na ‘yan sanda, IGP USMAN ALKALI BABA na barin zurfafan tsarin dimokuradiyya da ingantaccen tsarin zabe a kasar nan.
“Daga watan Janairu zuwa yau, jami’an ‘yan sanda sun gudanar da sintiri na dabara da leken asiri, da kai samame a maboyar ‘yan ta’adda, ayyukan ceto, tasha da bincike, aikin ‘yan sandan al’umma, da hada kai da masu ruwa da tsaki da dai sauransu.
“Wadannan ayyuka sun samar da sakamako mai kyau kuma an kama jimillar mutane 208 da ake zargi da hannu wajen garkuwa da mutane, fashi da makami, satar shanu da sauran laifuffukan ta’addanci, daga cikinsu an gurfanar da mutane 108 a gaban kotu,” inji shi.
CP ya ce bindigogin AK47 guda bakwai, bindigogin gida guda bakwai da kuma bindigogin Danish guda shida na daga cikin baje kolin da aka samu.