fidelitybank

An kama mutane 2 da zargin sace Basarake da Matarsa

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da laifin sace wani basarake, Abdulrahaman Ifabiyi, Onire na Owa-Onire, a karamar hukumar Ifelodun ta jihar a ranar Asabar da ta gabata da wasu mutane dauke da makamai suka yi.

Wadanda ake zargin: Bello Abubakar (31) da Bawa Seketri (30), ana tsare da su ne bisa zargin sace sarkin da matarsa ​​da direban sa ranar Asabar.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, Okasanmi Ajayi, a wata sanarwa da ya fitar a Ilorin ranar Lahadi, ya ce wadanda ake zargin suna taimakawa ‘yan sanda wajen gudanar da bincike kan lamarin.

Okasanmi, ya ce kokarin ceton da rundunar ta yi ne ya sa aka sako matar sarkin kuma ta sake haduwa da iyalanta.

Ya ce ana ci gaba da kokarin kubutar da sarkin da direban sa a hannun masu garkuwa da mutane.

Okasanmi ya ce, kwamishinan ‘yan sandan, Paul Odama ne ya aike da tawagar ‘yan sandan dabarun yaki tare da ‘yan banga da mafarauta zuwa yankin nan take, tare da ba da umarnin kubutar da wadanda abin ya shafa tare da kamo wadanda suka aikata laifin.

legit breaking news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Hisbah za ta yi wa ‘yan Daban Kano aure

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da wani...

Ganduje ya dawo Najeriya bayan ya shafe wata guda a Landan

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje,...

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi sabon shugaba

Farfesa Haruna Musa, ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Bayero...

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa...

Gwamnatin Tinubu na takalar Kwankwaso da fada – Buba Galadima

Jigo a jam'iyyar NNPP, kuma na hannun tsohon gwamnan...

Newcastle United ta dauki dan wasan tsakiya Jacob daga Aston Villa

Newcastle United ta sanar da daukar dan wasan tsakiya...

Hisba ta kama ‘yan Mata 62 da zargin aikata baɗala a Kano

Hukumar Hisbah ta kama mutane 62 kan zargin aikata...
X whatsapp