fidelitybank

An kama mutane 19 da zargin tare motar shinkafa a Kano

Date:

Kimanin mutane 19 da ake zargin sun wawure wata motar shinkafa a ranar Lahadi a Kano sun shiga hannun jami’an hukumar tsaron farin kaya ta NSCDC reshen jihar Kano.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan DSC Ibrahim Idris-Abdullahi, a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya bayyana cewa wadanda ake zargin sun kai harin ne a kan hanyar Kano zuwa Zariya.

A cewarsa, motar da ke dauke da daruruwan buhunan shinkafa mai nauyin kilogiram 50 daga kamfanin Alhamsad Rice Mill da ke Sharada a Kano, tana da rajista mai lamba UGG 532 XA.

Ya kara da cewa ‘yan bindigar sun far wa motar ne suka yi awon gaba da buhunan shinkafa, inda ya jaddada cewa motar ta nufi Zariya a jihar Kaduna.

DSC Ibrahim Idris-Abdullahi ya ce, “Da samun rahoton, jami’an NSCDC sun yi gaggawar tura jami’ansu zuwa wurin, inda suka kama wadanda ake zargin sannan an kwato musu buhunan shinkafa 29.”

Ya ce an kubutar da direban babbar motar da mataimakansa ba tare da wani rauni ba, yana mai tabbatar da cewa za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike.

bbc news nigeria today live

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp