fidelitybank

An kama mutane 15 a Anambra yayin wani arangama da ‘yan sanda

Date:

Kimanin mutane 15 ne aka kama a yankin Aguleri da ke karamar hukumar Anambra ta Gabas, mahaifar tsohon gwamna, Cif Willie Obiano.

Kamen ya biyo bayan wata arangama da aka yi tsakanin ‘yan kungiyar asiri da jami’an ‘yan sanda a yankin.

Wata majiya ta ce wasu ‘yan bindiga dauke da bindigu ne suka mamaye al’ummar garin da misalin karfe 11 na safiyar Lahadi inda suka fara harbin kan mai uwa da wabi, lamarin da ya sa mazauna garin suka tsere.

Ana zargin ‘yan bindigar ‘yan kungiyar asiri ne da ke fafatawa da wata kungiyar da ke hamayya da juna. Jami’an ‘yan sanda ne suka shiga tare da yi musu artabu da bindiga.

Wata majiya ta ce ba a samu asarar rai ba amma mutane da dama sun samu raunuka daban-daban sakamakon harbin.

Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Anambra, Ikenga Tochukwu ya tabbatar da faruwar lamarin.

Sai dai ya musanta ikirarin cewa ‘yan sanda sun jikkata, ya kara da cewa an kama wasu daga cikin ‘yan kungiyar asiri.

A cewar PPRO: “An shawo kan lamarin, bisa umarnin kwamishinan ‘yan sanda, Echeng Echeng. Mataimakin kwamishinan ‘yan sanda mai kula da ayyuka ya jagoranci jami’an ‘yan sanda zuwa wurin tare da hana matasan farmaki ofishin ‘yan sanda.”

Ya tabbatar da cewa an kama sama da mutane 15 yayin da aka kwato wasu muggan makamai.

Ya kuma tabbatar da cewa, ‘yan sanda na lalubo hanyoyin warware rikicin, ciki har da yin kira da a yi sulhu a tsakanin matasan da suka fusata.

“Mun kuma tsananta sintiri a yankin, da nufin inganta zaman lafiya da tsaro,” in ji shi.

nigeria news(punch)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp