fidelitybank

An kama mutane 149 da suka addabi al’ummar Kano

Date:

Rundunar ƴan sanda a Kano ta ce, ta kama mutum 149 saboda zarginsu da ayyukan fashi da makami da daba da garkuwa da mutane da sauran miyagun laifuka cikin kwanaki 10 da suka gabata.

Kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna ne ya bayyana haka a lokacin da yake magana da manema labarai game da kamen da rundunar ta yi.

Ya ce an kama ƴan daba 106 da waɗanda ake zargi masu fashi da makami ne su 25 da mutum biyu da ake zargi suna garkuwa da mutane sai masu satar mota uku da dillalan miyagun ƙwayoyi uku a sassa daban-daban na jihar.

“Mun kuma gano motoci biyu da babura takwas da wuƙaƙe 58 da bindiga ɗaya da ƙunshi 87 na abin da ake zargin tabar wiwi ne.

Kiyawa ya ce kamen ya biyo bayan shawagin da ƴan sanda suke yi a sassan jihar domin hana aikata laifuka.

A cewarsa, mutanen da aka kama na sashen binciken manyan laifuka na rundunar inda ake gudanar da bincike a kan su.

Kwamishinan ƴan sanda na jihar, Salman Dogo Garba ya ce rundunar za ta ci gaba da aiki ba dare ba rana domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

vanguardnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp