fidelitybank

An kama mutane 143 bisa zargin garkuwa da mutane a Kaduna

Date:

Rundunar yan sanda a jihar Kaduna ta tabbatar da kamen mutum 143 da ake zargi masu satar mutane ne da kuma yan fashi a wurare daban daban na jihar a tsukin wata biyu.

Kwamishinan yan sandan jihar, Audu Dabigi ne ya bayyana haka a wata hira da ya yi da manema labarai a hedikwatar rundunar inda ya ce an gano wasu manyan makamai daga hannun mutanen.

Mutanen da aka kama sun hada da yan fashi 73 sai yan bindiga 70 ciki har da wanda ake nema ruwa a jallo da aka damke a lokacin da yake kokarin hada wa yan bindigar wani tsubbu domin gudanar da ayyukansu.

Ya kara da cewa yan sandan sun halaka yan bindiga tara cikin wata biyu da suka gabata.

Dabigi ya ce cikin makaman da aka gano a hannun mutanen da ake zargi sun hada da bindiga kirar AK47 da wasu bindiga kirar gida da kuma alburusai da dama.

Ya kara da cewa an sake kama mutum 985 da ake zargi masu satar waya ne da yan fashi takawas da kuma wani da ake zargi da satar kaya a tashar jirgin kasa.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp