fidelitybank

An kama Mutane 12 bayan sun kashe Matashi da wuƙa a Masallaci lokacin Sallar dare

Date:

Rundunar ‘yansada reshen jihar Kaduna ta ce, ta kama mutum 12 da zargin kai hari masallaci a Kaduna da ke arewacin ƙasar.

Wata sanarwa da kakakin rundunar a Kaduna, DSP Mansur Hassan, ya fitar ta ce harin ya yi sanadin kashe wani matashi mai suna Usman Mohammad mai shekara 23.

A cewar DSP Mansur, rundunar ‘yansandan ta samu rahoto daga wani mazaunin yankin Rigasa cewa ‘yandaba ɗauke da makamai na shirin kai hari kan masu sallar Tahajjud.

“Da jin rahoton ne kuma dakaru suka bazama amma kafin su ƙarasa har sun daɓa wa wani matashi mai suna Usman Mohammed wuƙa, wanda likita ya tabbatar da mutuwarsa a asibiti,” in ji shi.

Ya ce sun isa wurin ne bisa rakiyar dakarun sa-kai na Civilian Joint Task Force (CJTF), kuma tuni sun ƙaddamar da cikakken bincike kan lamarin.

legit breaking news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp