Rundunar ‘yan sandan Jihar Edo, ta ce, ta kama jimillar mutum 102 da take zargi da aikata garkuwa da mutane cikin shekarar 2022.
Kazalika, an ceto mutum 68 da aka yi garkuwa da su, a cewar kakakin rundunar Chidi Nwabuzor cikin wata sanarwa a yau Asabar.
Sanarwar ta ƙara da cewa dakaru sun kashe mutum 58 sannan sun kama 65 da ake zargi da aikata fashi da makami.
Haka nan, an kama wasu 64 da ake zargi da kisan kai, 193 bisa zargin shiga ƙungiyoyin asiri, da kuma 19 kan aikata fyaɗe da kuma lalata.
Cikin makaman da suka yi nasarar ƙwacewa akwai bindigogi ƙirar Ak-47, da harba-ruga 11, da ƙananan bindigogi ƙirar gida 69.