fidelitybank

An kama Matashin da ya yo garkuwa da kansa a Legas

Date:

Rundunar ‘yan sanda jihar Legas ta ce, ta kama wani matashi kan zargin ƙaryar garkuwa da kansa.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar, Benjamin Hundeyin, ne ya bayyana haka a shafinsa na X, a lokacin da yake tsokaci kan wani saƙo da wani matashi da ke amfani da shafin mai suna @Flacko ya wallafa a shafin.

FlackoT ya wallafa cewa an tsare shi a ofishin ‘yan sanda na Ikeja kan zargin garkuwa da wani mutum da bai san komai game da shi ba.

”Jama’a an tsare ni a ofishin ‘yan sanda. Bani da isasshen lokaci, kuma ban san abin da zan yi ba, wannan ita ce kawai hanyar da zan bayyana wa duniya halin da nake ciki, saboda ku san halin da nake ciki,” kamar yadda matashin ya wallafa.

“Wani ne ya yi ƙaryar garkuwa da kansa, ya kuma buƙaci kuɗin fansa daga wajen mahaifinsa, mahaifin nasa ya kai rahoto wajen ‘yan sanda, inda su kuma suka bibiyi wayata, wllh ba abin da na sani game da batun har sai da na isa ofishin ‘yan sandan”.

Yayin da yake mayar da martani kan saƙon matashin, mai magana da yawun ‘yan sandan na Legas, Hundeyin ya ce binciken ‘yan sanda ya gano cewa wani matashi ne mai shekara 20 ya yi ƙaryar garkuwa da kansa. Inda aka riƙa kira mahifisna da lambobi daban-daban domin neman kuɗin fansa da yadda zai biya kuɗin.

“A ranar Alhamis ne jami’an bincike suka kai samame wani gida a unguwar Lekki inda suka samu Collins da wasu abokansa biyar da suka kwashe kwana 10 suna zaune a gidan”.

dailysun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp