Hukumar tsaro ta NSCDC a jihar Kano, ta kama wani matashi dan shekara 25 mai suna Alkasim Ya’u da laifin daba wa mahaifinsa wuka har lahira a Tudun Yola ‘C’ da ke karamar hukumar Gwale a jihar.
Kwamandan hukumar NSCDC, Mohammed Falala ne ya bayyana hakan a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Najeriya ta wayar tarho a Kano ranar Lahadi.
Ya ce lamarin ya faru ne a ranar Juma’a da misalin karfe 1:30 a gidan Alhaji Salisu Bala.
“Mahaifin marigayin, Alhaji Ya’u Mohammed, ya kawo dansa mai tabin hankali, Alkasim Ya’u, zuwa asibitin mahaukata na Dawanau, domin neman lafiya, inda suka nemi ganin likita a ranar Asabar, 6 ga watan Janairu,” inji shi.
Ya bayyana cewa, maimakon ya koma Katsina, marigayin ya yanke shawarar kwana a gidan dan uwansa a adireshin daya.
“Binciken da muka gudanar ya nuna cewa Alkasim ya kamu da tabin hankali ne sakamakon yadda yake gudanar da ayyukan ta’ammali da miyagun kwayoyi.
“A lokacin da suka isa Tudun Yola, dan mara lafiyar ya dauki wani abu mai kaifi ya raunata mahaifin, har sai da jami’an NSCDC da ke yankin suka shiga tsakani suka kai wanda aka kashen asibiti suka kama wanda ake zargin,” inji shi.
Ya ce ‘yan uwa suna shirye-shiryen mayar da gawar Katsina domin yi mata jana’iza, yayin da aka mika wanda ake zargin da baje kolin ga ofishin ‘yan sanda na Rijiyar Zaki domin ci gaba da bincike.