Wani matashi dan shekara 25 mai suna Adebowale ya shiga hannun jami’an hukumar Osun Amotekun bisa laifin satar babur.
Babur din, kamar yadda jami’an tsaro suka bayyana mallakar wani gida ne na unguwar Aratumi, a yankin Kelebe Osogbo.
Kwamandan rundunar ‘yan sandan Osun Amotekun, Birgediya Janar Bashir Adewinmbi ya ce jami’an tsaro ne suka kama Adebowale a lokacin da suke sintiri na yau da kullun bayan ya aikata hakan da misalin karfe 1 na safiyar Laraba.
Birgediya Janar Adewinmbi yayin da yake tabbatar da kamun a Osogbo a ranar Laraba, ya bayyana cewa an kama Adewale ne bayan ya saci babur TVS a unguwar Aratumi da ke Unguwar Kelebe a Osogbo.
“A cikin tafiyar da babur ne mutanen Amotekun da ke sintiri na yau da kullun suka gan shi suka kama mai laifin.
“Da aka yi masa tambayoyi, mai laifin ya amsa laifinsa.
“An mika shi ga ‘yan sanda don yi masa tambayoyi da kuma gurfanar da shi.”
Adewinmbi ya kuma gargadi masu aikata laifuka da su kaurace wa Osun.
“Ba ma daukar duk wani abu da ke da alaka da tsaron rayukan mutane da dukiyoyi da wasa. Muna aiki cikin hanzari kan duk wani yanki na bayanai da suka shafi tsaro don tabbatar da ko na gaskiya ne ko a’a.”
“Amotekun a shirye yake ya tona asirin masu aikata laifuka a wuraren da suke buya”. Adewinmbi ya tabbatar.
Ya bukaci mazauna yankin da su bayyana masu aikata laifuka a unguwannin su ga rundunar Amotekun domin dakile aikata laifuka a cikin al’umma.
A baya-bayan nan, babban birnin jihar Osun, Osogbo, ya sha fama da tashe-tashen hankulan da suka shafi laifuka, ci gaban ya kara matsin lamba ga gine-ginen tsaron jihar.
An samu rahoton yin garkuwa da mutane har a Osogbo babban birnin jihar.