fidelitybank

An kama matashi da zargin sace Solar a Jigawa

Date:

Jami’an hukumar tsaron NSCDC sun kama wani matashi mai shekaru 30 mai suna Inuwa Salisu bisa zarginsa da lalata da kuma satar batir masu hasken rana a jihar Jigawa.

Kakakin rundunar ‘yan sandan ASC Badrudeen Tijjani Mahmud ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai.

Ya ce an kama wanda ake zargin ne a ranar Juma’a a Gujungu, karamar hukumar Taura.

An kama shi ne a lokacin da yake niyyar jigilar batiran Roy solar da aka sace zuwa jihar Kano domin a zubar da shi.

Baturan da aka sata, wanda kudinsu ya kai N350,000, jami’an sa ido na NSCDC ne suka kama su.

Kwamandan NSCDC na jihar, Muhammad Danjuma, ya tabbatar da aniyarsa ta kare muhimman kadarori da ababen more rayuwa na kasa, inda ya sha alwashin gurfanar da wadanda ke yunkurin kawo cikas ga tsaron jama’a.

Ya bukaci jama’a da su sa ido tare da bayar da muhimman bayanai domin bunkasa kokarin jami’an tsaro na yakar miyagun laifuka.

Ya ce wanda ake zargin ya amsa laifinsa kuma za a gurfanar da shi a gaban kotun da ke da hurumin shari’a.

vangurd 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp