fidelitybank

An kama matasa 3 a Jigawa da zargin satar Batirin Solar

Date:

Hukumar tsaro ta NSCDC, a ranar Juma’a ta kama wasu mutane uku da ake zargi da satar batir masu amfani da hasken rana a jihar Jigawa.

Kakakin hukumar NSCDC, Adamu Shehu, ya bayyana haka a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai.

Ya ce jami’an NSCDC da ke garin Gujungu sun kama wadanda ake zargin ne a ranar Juma’a da karfe 2 na dare, kan zargin sata da hada baki da ya saba wa sashi na 286 da 96, wanda hukuncinsa a sashi na 96 da 97.

Shehu ya zargi mutanen ukun Umar Adam Abdullahi, Kabiru M. Musa, da Shafi’u Hamza da satar batura masu amfani da hasken rana a kan hanyar Hadejia, cikin garin Gujungu. Ma’aikatar ayyuka ta jihar Jigawa ce ta sanya fitilun titunan da nufin haskaka garin da kuma samar da tsaro.

Shehu ya ce an kama wadanda ake zargin ne da hannu wajen aikata laifin.

A cewarsa: “An kama su ne da batirin Roy 12V/150Ah mai amfani da hasken rana da kuma na’urar caji da aka cire daga jikin fitilar titin, wanda kudinsa ya kai Naira 320,000.”

Ya ce bincike ya nuna cewa a cikin jimillar fitilun masu amfani da hasken rana guda 130 da ke kan manyan titunan garin, 23 an sace musu batir.

Ya tabbatar da cewa wadanda ake zargin sun amsa laifin da aka aikata kuma za a gurfanar da su a gaban kotu bayan an kammala bincike.

the nation newspaper 
today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp