fidelitybank

An kama Matasa 12 dauke da jabun dala dubu 56,300

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Gombe ta kama wasu mutane 12 da ke da alaka da wasu kungiyoyin jabu guda biyu da ke gudanar da ayyukansu a jihar.

Wadanda ake zargin, shida ne daga kowace kungiya, an same su da kudi dalar Amurka $56,300 na jabun dalar Amurka da kuma naira 265,000 na jabun kudin Najeriya.

A cewar rundunar ‘yan sandan, dukkanin kungiyoyin biyu sun kware wajen kera takardun jabu na dalar Amurka da kuma Nairar Najeriya.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Mahid Abubakar, ya bayyana cewa, an gudanar da kamen ne a wurare daban-daban, da ya shafi kananan hukumomin Bajoga, Funakaye da Dukku na jihar Gombe.

A cewar PPRO, an kama ‘ya’yan daya daga cikin kungiyoyin da wasu jabun daloli 500 na dala 100 da kuma N265,000.

Mahid ya bayyana cewa an yi musu dirar mikiya ne bayan da wani Buba Muhammadu ya yi kokarin siyan kwaya daga hannun wani Muhammad Ismail da ke unguwar Sangaru da ke garin Bajoga da kudin jabu na Naira 1,000, inda ya bayyana cewa kama Muhammadu ya kai ga kama wasu ‘yan kungiyar.

Ya bayyana sunayen wadanda ake zargin na farko da suka hada da Buba Muhammadu mai shekaru 45, Jungudo Muhammadu (53), Adamu Yusuf Mallum (30), Abdulhamid Abdullahi (60), Salihu Abdulhamid (50), da Abubakar Abdullahi (35).

An gudanar da bullar kungiyar ta biyu a kauyen Malala da ke karamar hukumar Dukku.

Mahid ya bayyana na biyun wadanda ake zargin “Haruna Adamu mai shekaru 60,  dan kauyen Tanji dake karamar hukumar Darazo ta jihar Bauchi; Garba Ibrahim, dan shekara 25, Hashidu, karamar hukumar Dukku, Jihar Gombe; Samaila Musa, mai shekara 30, Gombe Abba, karamar hukumar Dukku; Sa’adu Muhammed, mai shekara 23, mai lamba 10 Badarawa Quarters, Jihar Kaduna; Yusuf Abdullahi, dan shekara 30, Gombe Abba, karamar hukumar Dukku; Muhammadu Umaru, mai shekara 26, na karamar hukumar Gombe Abba Dukku”.

Ya ce duk wadanda ake zargin sun amsa laifinsu a cikin ayyukan jabun kuma za su fuskanci shari’a a kan haka.

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...
X whatsapp