fidelitybank

An kama Matar da ake zargi da kashe dan kishiyarta da guba a Kaduna

Date:

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna ta ce, ta kama da tsare wata mata mai suna Zaliha Shu’aibu bisa zargin kashe ɗan kishiyarta ɗan wata uku da haihuwa da maganin ƙwari.

A wata sanarwa da kakakin rundunar ƴansandan jihar ta Kaduna, DSP Mansur Hassan ya fitar, al’amarin ya faru ne a ranar 13 ga watan nan na Mayu a gidansu da ke ƙauyen Malari a ƙaramar hukumar Soba.

Sanarwar ta ce shaidu sun ce uwar yaron dai ta fita daga ɗakinta domin shiga banɗaki lokacin da kishiyar tata ta shigar mata ɗaki kuma bayan ta koma ɗakin ne ta ga kishiryar rungume da ɗan nata.

Bayan ta miƙa mata jaririn ne sai uwar ɗan ta fahimci yadda kumfa ke fita daga bakin yaron nata sannan kuma akwai rauni a wuyansa, inda yaron ya kece da kuka.

Bayan bincike, rundunar ƴansandan ta ce matar ta tabbatar da cewa ta aikata laifin ne da taimakon ƙanen mijinta wanda shi shi ne ya bata gubar da ta yi amfani a kan jaririn. Ƙanen mijin dai ya gudu ba a kai ga kama shi ba tukunna.

latest news in nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp