Rundunar ƴansandan jihar Kaduna ta ce, ta kama da tsare wata mata mai suna Zaliha Shu’aibu bisa zargin kashe ɗan kishiyarta ɗan wata uku da haihuwa da maganin ƙwari.
A wata sanarwa da kakakin rundunar ƴansandan jihar ta Kaduna, DSP Mansur Hassan ya fitar, al’amarin ya faru ne a ranar 13 ga watan nan na Mayu a gidansu da ke ƙauyen Malari a ƙaramar hukumar Soba.
Sanarwar ta ce shaidu sun ce uwar yaron dai ta fita daga ɗakinta domin shiga banɗaki lokacin da kishiyar tata ta shigar mata ɗaki kuma bayan ta koma ɗakin ne ta ga kishiryar rungume da ɗan nata.
Bayan ta miƙa mata jaririn ne sai uwar ɗan ta fahimci yadda kumfa ke fita daga bakin yaron nata sannan kuma akwai rauni a wuyansa, inda yaron ya kece da kuka.
Bayan bincike, rundunar ƴansandan ta ce matar ta tabbatar da cewa ta aikata laifin ne da taimakon ƙanen mijinta wanda shi shi ne ya bata gubar da ta yi amfani a kan jaririn. Ƙanen mijin dai ya gudu ba a kai ga kama shi ba tukunna.