fidelitybank

An kama mata biyu da ake zargi sun sato jarir ɗanye shagaf

Date:

Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Ogun, sun cafke wasu mata biyu, bisa zargin satar wani jariri dan mako daya a jihar Ogun.

Rahotanni sun ce, jami’an ‘yan sandan sun kama matan ne a ranar 25 ga watan Yuli, bayan da aka ga daya daga cikin wadanda ake zargin mai suna Chinyere Nwozu ‘yar shekaru 53 tare da jaririyar da misalin karfe 9 na safe a wannan rana, kuma hakan ya haifar da shakku a tsakanin mazauna garin, saboda ta kasa shayar da yaro nono.

Nan take mazauna yankin suka kai rahoton lamarin zuwa shelkwatar sashin Sango Ota kuma an tura wasu jami’an bincike don kama Nwozu.

A yayin da ake yi mata tambayoyi, ta ce, ta sayi yaron ne a hannun wata Ngozi Akaeme da ke zaune a unguwar Agege a jihar Legas kan kudi Naira 500,000.

Karanta wannan: Ana zargin Matashi da satar Lasifikar Massalaci da Janerata

Kakakin rundunar ‘yan sandan Ogun, Abimbola Oyeyemi ya ce, “Da samun wannan labarin, DPO na Sango Ota, SP Dahiru Saleh, ya yi karin bayani ga jami’an bincikensa zuwa wurin da aka kama matar.”

Bayan kama Akaeme, ta bayyana cewa “ta yi shawarwari da mahaifiyar jaririn da ta amince ta sayar da jaririn.”

A cewar kakakin na jihar Ogun, sun kasa gano mahaifiyar yaron.

Oyeyemi ya bayyana cewa kwamishinan ‘yan sanda, CP Lanre Bankole, ya bayar da umarnin a mika wadanda ake zargin zuwa hukumar CIID ta jihar, domin ci gaba da bincike tare da gurfanar da su gaban kuliya.

vanguard news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp