fidelitybank

An kama mata biyu da ake zargi sun sato jarir ɗanye shagaf

Date:

Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Ogun, sun cafke wasu mata biyu, bisa zargin satar wani jariri dan mako daya a jihar Ogun.

Rahotanni sun ce, jami’an ‘yan sandan sun kama matan ne a ranar 25 ga watan Yuli, bayan da aka ga daya daga cikin wadanda ake zargin mai suna Chinyere Nwozu ‘yar shekaru 53 tare da jaririyar da misalin karfe 9 na safe a wannan rana, kuma hakan ya haifar da shakku a tsakanin mazauna garin, saboda ta kasa shayar da yaro nono.

Nan take mazauna yankin suka kai rahoton lamarin zuwa shelkwatar sashin Sango Ota kuma an tura wasu jami’an bincike don kama Nwozu.

A yayin da ake yi mata tambayoyi, ta ce, ta sayi yaron ne a hannun wata Ngozi Akaeme da ke zaune a unguwar Agege a jihar Legas kan kudi Naira 500,000.

Karanta wannan: Ana zargin Matashi da satar Lasifikar Massalaci da Janerata

Kakakin rundunar ‘yan sandan Ogun, Abimbola Oyeyemi ya ce, “Da samun wannan labarin, DPO na Sango Ota, SP Dahiru Saleh, ya yi karin bayani ga jami’an bincikensa zuwa wurin da aka kama matar.”

Bayan kama Akaeme, ta bayyana cewa “ta yi shawarwari da mahaifiyar jaririn da ta amince ta sayar da jaririn.”

A cewar kakakin na jihar Ogun, sun kasa gano mahaifiyar yaron.

Oyeyemi ya bayyana cewa kwamishinan ‘yan sanda, CP Lanre Bankole, ya bayar da umarnin a mika wadanda ake zargin zuwa hukumar CIID ta jihar, domin ci gaba da bincike tare da gurfanar da su gaban kuliya.

latest news 
in nigeria today 2021 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp