fidelitybank

An kama masu zanga-zanga 9 a Borno sakamakon rike tutar Rasha

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Borno, ta tabbatar da cafke wasu masu zanga-zanga 9 bisa zargin nuna tutar kasar Rasha a Maiduguri.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Yusuf Lawal ne ya bayyana haka yayin da yake bayar da rahoton halin da ake ciki a ranar Talata a Maiduguri, babban birnin jihar.

Ya ce an kama wadanda ake zargin ne a unguwar Zannari Tamsu da ke unguwar Gwange, Maiduguri a ranar 5 ga Agusta, 2024.

Lawal ya ce wadanda aka kama sun hada da Khalafi Abdulhamid, Mohammed Abubakar, Mohamed Ibrahim, da Abba Hassan dukkansu mazauna yankin Zannari Tamsu.

“Bugu da kari, an kama wasu masu zanga-zanga biyar a unguwar Bulumkutu da ke Maiduguri, dauke da tutocin kasar Rasha.

“Wadanda ake zargin, Bashir Ahmad, Musa Lawan, Abba Mallam, Habibu Auwal, da Inusa Abdullahi, an mika su zuwa Crack Squad domin gudanar da bincike mai zurfi, tare da gurfanar da su a gaban kotu,” in ji shi.

Kwamishinan ya ce an kwantar da hankulan muzaharar inda ya ce ‘yan sanda za su ci gaba da sanya ido da kuma sintiri a yankin domin tabbatar da tsaron lafiyar jama’a.

daily post today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp