fidelitybank

An kama masu garkuwa da fashi har su 15

Date:

Rundunar ‘yansanda ta ce, ta kama Mutum 15 da take zargi da aikata fashi da kuma garkuwa da mutane a faɗin ƙasar.

Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, Olumiyiwa Adejobi ya ce dakarunsu sun yi nasarar ƙwace makamai da dama.

Sanarwar ta ce rundunarta ta Special Tactical Squad (STS) ce da taimakaon mafararuta da ‘yan sa-kai ta yi nasarar kama ‘yanfashi huɗu a jihar Taraba ranar 25 ga watan Afrilu, sannan ta ƙwace bindigogi uku.

A jihar Kaduna kuma, wani samame da dakaru suka kai ya yi sanadiyyar kama mutum biyar da zargin aikata fashi. An kama ɗauke da bindigogi ƙirar AK-49 da AK-47 huɗu.

“A ranar 17 ga watan Afrilun kuma, dakarun sun kama wani mai suna Isa Ibrahim, wanda ya amsa cewa ya koma Kaduna ne domin kafa wata sabuwar dabar ‘yanfashi bayan kama abokan aikinsa a jihar Kwara,” in ji sanarwar.

“Ranar dai, samamen da jami’ai suka kai a ƙauyen Lamido ya yi nasarar kama ‘yanfashi biyu, waɗanda suka amsa laifukan fashi.

“A ranar 18 ga watan, ‘yansandan jihar [Kaduna] sun kama wasu masu safarar bindigogi ɗauke da binidigogin AK-47 biyu, daga baya kuma suka kama wani ɗauke da bindigogi biyu ƙirar gida da wata doguwar sarƙa a cikin buhu.”

nasarawa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp