Rundunar ‘yansanda ta ce, ta kama Mutum 15 da take zargi da aikata fashi da kuma garkuwa da mutane a faɗin ƙasar.
Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, Olumiyiwa Adejobi ya ce dakarunsu sun yi nasarar ƙwace makamai da dama.
Sanarwar ta ce rundunarta ta Special Tactical Squad (STS) ce da taimakaon mafararuta da ‘yan sa-kai ta yi nasarar kama ‘yanfashi huɗu a jihar Taraba ranar 25 ga watan Afrilu, sannan ta ƙwace bindigogi uku.
A jihar Kaduna kuma, wani samame da dakaru suka kai ya yi sanadiyyar kama mutum biyar da zargin aikata fashi. An kama ɗauke da bindigogi ƙirar AK-49 da AK-47 huɗu.
“A ranar 17 ga watan Afrilun kuma, dakarun sun kama wani mai suna Isa Ibrahim, wanda ya amsa cewa ya koma Kaduna ne domin kafa wata sabuwar dabar ‘yanfashi bayan kama abokan aikinsa a jihar Kwara,” in ji sanarwar.
“Ranar dai, samamen da jami’ai suka kai a ƙauyen Lamido ya yi nasarar kama ‘yanfashi biyu, waɗanda suka amsa laifukan fashi.
“A ranar 18 ga watan, ‘yansandan jihar [Kaduna] sun kama wasu masu safarar bindigogi ɗauke da binidigogin AK-47 biyu, daga baya kuma suka kama wani ɗauke da bindigogi biyu ƙirar gida da wata doguwar sarƙa a cikin buhu.”