fidelitybank

An kama mai baiwa ‘yan bindiga kudi a Zamfara

Date:

Rundunar jami’an NSCDC reshen jihar Zamfara, ta ce, jami’anta sun kama wani ma’aikacin POS mai suna Mustapha bisa zargin yin hada-hadar kudi a madadin ‘yan bindiga.

Kwamandan jihar, Muhammad Bello Muazu, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin, ya ce an kama mai laifin ne a yayin da yake yin wannan ciniki a yankin Birnin Tsaba da ke karamar hukumar Zurmi ta jihar.

Ya ce ‘yan sandan sun kwato injinan POS guda biyu, inda ya kara da cewa wanda ake zargin ya amsa cewa wani shugaban ‘yan fashi ne ya saya masa injinan.

Ya bayyana cewa wanda ake zargin ya amsa cewa yana amfani da na’urar POS ne kawai wajen yin kasuwanci a madadin ‘yan fashin da yake karewa.

“A yayin da ake yi masa tambayoyi, wanda ake zargin ya shaida mana cewa sun buga masa waya daga dajin inda suka umarce shi da ya karbi kudi a madadinsu ya ajiye kudin a wurinsa.” Yace

A cewarsa, idan ‘yan fashi suna son siyan magunguna, man fetur ko kayan abinci, sai su tura wani kai tsaye wurin wanda ake zargin ya karbi kudin ya saya musu duk abin da suke so.

“Daga lura da muka yi, hakan zai shafi yadda ‘yan fashin ke amfani da POS na karkara wajen hada-hadar kasuwanci. Ma’aikatan POS na karkara sun fi kusa da masu aikata laifuka,” ya bayyana

daily post nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp