fidelitybank

An kama Kwamandan da ya yi sanadin kisan Gulak

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Imo da ke kudu maso gabashin Najeriya ta yi holen wani kwamandan IPOB da ta daɗe tana nema ruwa a jallo mai suna Chinwendu Nwangwu wanda aka fi sani da Onyearmy bayan da ta samu nasarar kama shi.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Michael Abattam, ya ce an kama mista Nwaagwu wanda ya bar aiki a rundunar sojin Najeriya shekara takwas da suka gabata a yankin ƙaramar hukumar Aboh Mbaise da ke jihar.

Mista Abattam ya ce tsohon sojan mai shekara 34 ya aikata laifuka da dama ciki har da kashe-kashen mutane, da kai hare-hare ofisoshin zaɓe a jihar.

Rundunar ‘yan sanadn jihar ta ce bayan da ta binciki gidansa ta samu bindigogi biyar, da wasu manyan bindigogin, da ƙananan bindigogi ƙirar gida, da gidan alburusai 50, da gurneti tara ƙirar gida.

Haka kuma mista Nwangwu ya amsa laifin bai wa jami’an ƙungiyar ‘yan aware da ESN kusan 1,000 horon makamai da dabarun harin ta’addanci.

Sannan kuma mista Onyearmy ya amince cewa ya jagoranci hare-hare da dama a jihar musamman kan jami’an tsaro da ofisoshin ‘yan sanda da na hukumar zaɓe a jihar.

Ya kuma bayyana yadda ya shirya harin da ya yi sanadin mutuwar Ahmed Gulak, mai bai wa tsohon shugaban ƙasar Goodluck Jonathan kan harkokin siyasa.

daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp