fidelitybank

An kama Kwamandan da ya yi sanadin kisan Gulak

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Imo da ke kudu maso gabashin Najeriya ta yi holen wani kwamandan IPOB da ta daɗe tana nema ruwa a jallo mai suna Chinwendu Nwangwu wanda aka fi sani da Onyearmy bayan da ta samu nasarar kama shi.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Michael Abattam, ya ce an kama mista Nwaagwu wanda ya bar aiki a rundunar sojin Najeriya shekara takwas da suka gabata a yankin ƙaramar hukumar Aboh Mbaise da ke jihar.

Mista Abattam ya ce tsohon sojan mai shekara 34 ya aikata laifuka da dama ciki har da kashe-kashen mutane, da kai hare-hare ofisoshin zaɓe a jihar.

Rundunar ‘yan sanadn jihar ta ce bayan da ta binciki gidansa ta samu bindigogi biyar, da wasu manyan bindigogin, da ƙananan bindigogi ƙirar gida, da gidan alburusai 50, da gurneti tara ƙirar gida.

Haka kuma mista Nwangwu ya amsa laifin bai wa jami’an ƙungiyar ‘yan aware da ESN kusan 1,000 horon makamai da dabarun harin ta’addanci.

Sannan kuma mista Onyearmy ya amince cewa ya jagoranci hare-hare da dama a jihar musamman kan jami’an tsaro da ofisoshin ‘yan sanda da na hukumar zaɓe a jihar.

Ya kuma bayyana yadda ya shirya harin da ya yi sanadin mutuwar Ahmed Gulak, mai bai wa tsohon shugaban ƙasar Goodluck Jonathan kan harkokin siyasa.

leadership newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gobara na cigaba da lakume wasu yankunan Turai

Gobarar daji na ci gaba da ruruwa a sassan...

An kama Fursunoni 7 da suka tsere daga gidan kurkukun jihar Nasarawa

Hukumar kula da gidajen yari a Najeriya ta ce...

Gwamnati za ta gina titin jirgi a jihohi shida

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta haɗa gwiwa da...

Tinubu ya na cikin koshin lafiya – Farouk Adamu Aliyu

Tsohon ɗan majalisar wakilai daga jihar Jigawa, Faruk Adamu...

Amurka ta saka ladan dala miliyan biyar a kamo jagoran ‘yandaban Haiti

Amurka ta sanya dala miliyan biyar a matsayin lada...

Gwamnati ta janye karar da ta shigar kan Fasinjar jirgin Ibom

Gwamnatin Tarayya ta janye ƙarar da ta shigar kan...

Na so komawa Manchester United a 2012 – Lwandowski

Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya...

Isak ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar...

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

Ɗanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded...

Atiku zai iya guduwa daga ADC ya koma PDP idan Jonathan ya tsaya takara – Diran

Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa,...

Zoben matar Ronaldo ya kai dala miliyan 5 – Masana

Masana sun yi kiyasin tsadar zoben da Cristiano Ronaldo...

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama...
X whatsapp