Daya daga cikin masu laifin da suka tsere daga gidan yarin Kuje lokacin da ‘yan ta’adda suka kai hari a ranar 5 ga Yuli, 2022, an kama Salisu Buhari a jihar Nasarawa.
A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa, DSP Ramhan Nansel ya fitar, ya ce an kama Buhari ne tare da wani mutum da ake zargi da aikata laifin mai suna Zubairu Ali a karamar hukumar Nasarawa da ke jihar bisa laifin yin fashi.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Jami’an ‘yan sanda da ke aiki da sashin Nasarawa a wani samame da suka kai sun kama wasu biyu Zubairu Ali 27yrs da Salisu Buhari 24yrs bisa laifin satar babura a karamar hukumar Nasarawa ta jihar Nasarawa.
“Bincike na farko ya nuna cewa wadanda ake zargin sune ke da alhakin mafi yawan satar babura a karamar hukumar Nasarawa da kewaye.
“Da aka yi masa tambayoyi, Salisu Buhari ya amsa cewa ya tsere daga gidan yarin Kuje lokacin da aka kai wa gidan hari a shekarar da ta gabata, tare da alakanta shi da mukarrabansa, kuma ya shiga harkar aikata laifuka.”
A cewar sanarwar, kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Maiyaki Baba ya bayar da umarnin mika karar zuwa sashin binciken manyan laifuka na jihar, Lafia, domin gudanar da cikakken bincike.