fidelitybank

An kama guda daga cikin wanda suka tsere daga kurkukun kuje

Date:

Daya daga cikin masu laifin da suka tsere daga gidan yarin Kuje lokacin da ‘yan ta’adda suka kai hari a ranar 5 ga Yuli, 2022, an kama Salisu Buhari a jihar Nasarawa.

A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa, DSP Ramhan Nansel ya fitar, ya ce an kama Buhari ne tare da wani mutum da ake zargi da aikata laifin mai suna Zubairu Ali a karamar hukumar Nasarawa da ke jihar bisa laifin yin fashi.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Jami’an ‘yan sanda da ke aiki da sashin Nasarawa a wani samame da suka kai sun kama wasu biyu Zubairu Ali 27yrs da Salisu Buhari 24yrs bisa laifin satar babura a karamar hukumar Nasarawa ta jihar Nasarawa.

“Bincike na farko ya nuna cewa wadanda ake zargin sune ke da alhakin mafi yawan satar babura a karamar hukumar Nasarawa da kewaye.

“Da aka yi masa tambayoyi, Salisu Buhari ya amsa cewa ya tsere daga gidan yarin Kuje lokacin da aka kai wa gidan hari a shekarar da ta gabata, tare da alakanta shi da mukarrabansa, kuma ya shiga harkar aikata laifuka.”

A cewar sanarwar, kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Maiyaki Baba ya bayar da umarnin mika karar zuwa sashin binciken manyan laifuka na jihar, Lafia, domin gudanar da cikakken bincike.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp