Rundunar ‘yan sandan jihar Legas, ta ce, jami’anta sun samu nasarar kama wasu gawartatun ‘yan fashi da makami, waɗanda ke ƙoƙarin guduwa bayan sun aikata fashin.
A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Benjamin Hundeyin, ya fitar ranar Asabar ya ce rundunar ta kama waɗanda ake zargin bayan da ta samu bayanan da ke cewa suna aikata fashi a kan haryar Ibeju zuwa Lekki.
Sanarwar ta ce bayan kama ‘yan fashi , an kuma kwato ƙananan bindigogi guda biyu, da kwanson zuba alburusai maƙare da alburusan , da manyan wayoyin hannu guda biyu.
Mista Hundeyin ya ce bayan fara gudanar da bincike ne kuma aka gano mutumin da ke sayar musu da makaman.
Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ya ce mutanen biyu, sun amsa cewa sun daɗe suna aikata fashi a wannan wuri, ya kuma ce za a gurfanar da su a gaban kotu da zarar an kammala bincike.