Mazauna yankin NEPA da ke karamar hukumar Jos ta Arewa a jihar Filato, sun kama wani da ake zargin mai garkuwa da mutane ne da ya karbi kudin fansa naira miliyan 1.5 daga hannun ‘yan uwan wadanda abin ya shafa.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Alabor Alfred, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce ana binciken wanda ake zargin a sashin yaki da masu garkuwa da mutane.
Wani dan banga a unguwar NEPA, wanda ya nemi a sakaya sunansa, a ranar Alhamis, ya ce bayan mazauna unguwar sun kama wanda ake zargin, nan take aka mika shi ga ’yan banga da ke yankin.
Ya kara da cewa daga baya an kai wanda ake zargin zuwa ofishin ‘yan sanda na Laranto.
Da yake bayyana lamarin, dan bangan ya ce wanda ya sace yaran ya yi garkuwa da yara biyu, daya mai shekaru hudu, dayan kuma mai shekaru biyar.
Sai dai a cewarsa bayan an biya kudin fansa naira miliyan 1.5, wanda ake zargin ya ki sakin yaran.
Dan bangan ya kara da cewa a lokacin da wanda ake zargin ya koma gidan da ba kowa a ciki inda yake ajiye yara kanana, masu wucewa suka ji kukan yaran, nan take suka garzaya zuwa ginin.
“Da isar sa sai mai garkuwa da mutanen da ke tare da kananan yara ya yi tsalle ta tagar, amma yayin da jama’a ke kururuwa da ihun ‘mai garkuwa da mutane,’ maza da mata daga cikin jama’a suka fito da yawa suka kama shi.
“Daga nan magidancin ya mika shi ga ’yan banga na al’umma inda suka kai shi ofishin ‘yan sanda na Laranto tare da kudi Naira 1,492,000 da ya karba daga iyayen wadanda abin ya shafa.” Inji mutumin.