Hukumar kare hakkin masu sayayya ta jihar Kano ta kwace kimanin buhun fulawa 487, da ta lalace a wajen ajiyar kaya a kasuwar Dawanau da ke birnin Kano.
Jaridar Punch a Najeriya ta ambato jami’in hulda da jama’a na hukumar Musbahu Yakasai a wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai, na cewa Daraktan riko na hukuma Dakta Baffa Dan’Agundi ne ya bayyana haka a ofishinsa bayan kwato fulawar.
Dakta Baffa Dan’Agundi ya ce, wasu mutanen kirki ne suka bai wa hukumar tasu bayanan sirri game da fulawar wacce aka kawo kasuwar da nufin sayar da ita. Ya kara da cewa gwajin da aka yi wa samfurin fulawar ya nuna cewa tuni ta dade da lalacewa.
Haka kuma ya ce, hukumar tasu ta kama lemuka masu yawan gaske da suka lalace kuma ake sayar da su a kasuwar Sabon Gari da ke jihar. Gwamnatin jihar Kano ta kwace buhun ‘lalatacciyar’ fulawa 487. In ji BBC.