fidelitybank

An kaiwa Malamin addini hari a Kano bayan an jikatasu da Matarsa

Date:

Wani malamin addinin Musulunci, Malam Kabir Idris, da matarsa sun jikkata sosai, bayan da wasu ‘yan bindiga suka kai musu farmaki a gidansu da ke unguwar Danrimi a yankin Rijiyar Lemo, a karamar hukumar Fagge, a daren Talata.

Malam Idris, wanda shi ne shugaban Madrasatul Kanzul Huda, ya bayyana cewa maharan sun shigo gidan sa yayin da yake barci, ba tare da satar waya ko babur da ke wajen gida ba. Ya ce, maimakon haka, sun yi musu barazana sannan suka kai musu hari da adda.

Idris ya samu raunuka guda shida a hannunsa da kuma guda biyu a kansa, yayin da matarsa ta samu raunuka biyu a hannunta.

Kungiyar Malaman Makarantun Addinin Musulunci ta Jihar Kano ta yi tir da wannan mummunan hari tare da kira ga hukumomin tsaro su binciki lamarin.

Yanzu haka Malam Idris na karɓar magani a Asibitin Kwararru na Murtala, sai dai an jinkirta yi masa tiyata saboda ƙarancin kuɗi.

vanguard new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...

Barau ya jagorancin gangamin zaben cike gurbi a Kano

Barau ya samu rakiyar Karamin Ministan Gidaje da Raya...

Gwamnatin Kano ta kara fadada shirin matasa 

Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya sake,...

An kaiwa Malamin addini hari a Kano bayan an jikatasu da Matarsa

Wani malamin addinin Musulunci, Malam Kabir Idris, da matarsa...

Kotun Kano ta daure wata Mata da ake zargin ta tsafe su

Kotun Majistiri mai lamba 7 da ke Nomansland, ƙarƙashin...

Dalibi ya kashe kansa a cikin Jami’a

Hukumar jami'ar Obafemi Awolowo da ke jihar Osun, sun...

Gobara na cigaba da lakume wasu yankunan Turai

Gobarar daji na ci gaba da ruruwa a sassan...

An kama Fursunoni 7 da suka tsere daga gidan kurkukun jihar Nasarawa

Hukumar kula da gidajen yari a Najeriya ta ce...

Gwamnati za ta gina titin jirgi a jihohi shida

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta haɗa gwiwa da...

Tinubu ya na cikin koshin lafiya – Farouk Adamu Aliyu

Tsohon ɗan majalisar wakilai daga jihar Jigawa, Faruk Adamu...

Amurka ta saka ladan dala miliyan biyar a kamo jagoran ‘yandaban Haiti

Amurka ta sanya dala miliyan biyar a matsayin lada...

Gwamnati ta janye karar da ta shigar kan Fasinjar jirgin Ibom

Gwamnatin Tarayya ta janye ƙarar da ta shigar kan...
X whatsapp