fidelitybank

An kaiwa jami’in mu hari a gidansa na Kogi – INEC

Date:

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, ta tabbatar da cewa wasu ‘yan bindiga sun kai hari gidan Kwamishinan Zabe na Jihar Kogi.

Hukumar, a wata sanarwa da ta fitar a shafinta na X a ranar Juma’a, ta ce ‘yan bindigar sun kai hari gidan da karfe 3:30 na safiyar ranar Juma’a.

Ya ce ‘yan bindigar sun yi arangama da jami’an tsaron sama da mintuna 30 har sai da jami’an tsaro suka iso.

Ya kara da cewa ba a samu asarar rai ba yayin harin.

“Da sanyin safiyar yau Juma’a 1 ga watan Disamba, 2023, da misalin karfe 3:30 na safe, wasu ‘yan bindiga sun kai hari gidan kwamishinan zabe (REC) da ke Lokoja, jihar Kogi.

“Yayin da ba a yi asarar rayuka ba, an lalata dukiyoyi a rikicin da ya biyo baya. An tura tawagar jami’an tsaro hadin gwiwa don kare gidan. Wannan lamari dai ya faru ne kwana guda bayan da wasu gungun jama’a suka yiwa ofishin jahar mu kawanya.

“Muna kira da a gudanar da cikakken bincike tare da inganta tsaro ga ma’aikatanmu da kadarorinmu a jihar Kogi,” in ji INEC.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp