fidelitybank

An kai sumame shalkƙwatar Alƙalan wasa sakamakon zargin Barcelona ta miƙa na Goro

Date:

Ƴan sandan Sifaniya sun kai samame hedikwatar alƙalan wasan ƙasar a wani ɓangare na binciken zargin cin hanci da ake yi wa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barcelona.

Barcelona na fuskantar zargin cin hanci kan wasu kuɗaɗe da ta tura wa Jose Maria Enriquez Negreira, wani tsohon mataimakin shugaban kwamitin alƙalan wasan, don a dinga yi musu alfarma a wasanninsu.

Barcelona ta musanta zargin kuma ba a kama kowa ba a lokacin samamen a birnin Madrid.

An faɗa wa BBC Sport cewa alƙalin da ke sauraron shari’ar ya buƙaci a kwamatin alƙalan wasan mai suna Technical Committee of Referees (CTA) ya gabatar masa da wasu takardu.

Ba a kai takardun ba kuma dalilin da ya sa aka ɗauki matakin kai samamen ke nan a ranar Alhamis.

Tun farko, ofishin shigar da ƙara na Barcelona ne ya tayar da batun a watan Maris, inda ita ma hukumar ƙwallon Turai ta ƙaddamar nata binciken jim kaɗan bayan haka.

Ana zargin Barca ta biya Negreira da kamfaninsa Dasnil 95 yuro miliyan 8.4.

Ƙungiyar ta biya jimillar kuɗi yuro miliyan 1.4 tsakanin 2016 da 2018, kuma ta biya Negreira kusan miliyan bakwai tsakanin 2001 da 2018, wato shekarar da ya bar muƙaminsa da kwamitin alƙalan wasan.

assu update

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp