fidelitybank

An kai sumame shalkƙwatar Alƙalan wasa sakamakon zargin Barcelona ta miƙa na Goro

Date:

Ƴan sandan Sifaniya sun kai samame hedikwatar alƙalan wasan ƙasar a wani ɓangare na binciken zargin cin hanci da ake yi wa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barcelona.

Barcelona na fuskantar zargin cin hanci kan wasu kuɗaɗe da ta tura wa Jose Maria Enriquez Negreira, wani tsohon mataimakin shugaban kwamitin alƙalan wasan, don a dinga yi musu alfarma a wasanninsu.

Barcelona ta musanta zargin kuma ba a kama kowa ba a lokacin samamen a birnin Madrid.

An faɗa wa BBC Sport cewa alƙalin da ke sauraron shari’ar ya buƙaci a kwamatin alƙalan wasan mai suna Technical Committee of Referees (CTA) ya gabatar masa da wasu takardu.

Ba a kai takardun ba kuma dalilin da ya sa aka ɗauki matakin kai samamen ke nan a ranar Alhamis.

Tun farko, ofishin shigar da ƙara na Barcelona ne ya tayar da batun a watan Maris, inda ita ma hukumar ƙwallon Turai ta ƙaddamar nata binciken jim kaɗan bayan haka.

Ana zargin Barca ta biya Negreira da kamfaninsa Dasnil 95 yuro miliyan 8.4.

Ƙungiyar ta biya jimillar kuɗi yuro miliyan 1.4 tsakanin 2016 da 2018, kuma ta biya Negreira kusan miliyan bakwai tsakanin 2001 da 2018, wato shekarar da ya bar muƙaminsa da kwamitin alƙalan wasan.

nigeria news today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp