fidelitybank

An kai ni Birtaniya na yi aikatau amma na zama fitacce – Sir Mo farah

Date:

An shigar da Sir Mo Farah Birtaniya ne ba bisa ƙa’ida ba a lokacin da yake yaro aka tilasta masa yin aikatau a wani gida.

Fitaccen ɗan tseren Olympics din ya shaida wa BBC cewa waɗanda suka sace shi daga ƙasar Djibouti ne suka sanya masa suna Mohamed Farah.

Sunansa na ainihi Abdi Kahin. Yana da shekara tara a lokacin da wata mata da bai taɓa sani ba ta fitar da shi daga ƙasarsa ta gabashin Afrika. Sai ta kai shi aiki wani waje don ya dinga kula da ƴaƴan gidan, kamar yadda ya faɗa.

Ɗan tseren na tawagar Birtaniya ya ce “na yi ta ƙoƙarin dakatar da hakan, amma na kasa.”

A baya dai ɗan tseren ya taɓa cewa shi da iyayensa ƴan gudun hijirar Somaliya ne da suka tafi Birtaniya.

Amma a wani shiri na BBC da kamfanin Red Bull Studios da BBC News ta ganida aka yaɗa a ranar Laraba, ya ce iyayensa ba su taɓa zuwa Birtaniya ba.

Mahaifiyarsa da ƴan uwansa biyu na zaune ne a wata jiha a yankin Somaliland da ya ɓalle.

Mahaifinsa kuwa ya rasu ne sanadin harbinsa da aka yi tun Sir Mo yana ɗan shekara huɗu a duniya a wani rikici da aka yi a Somaliya.

A shekarar 1991 ne ƙasar Somaliland ta ayyana samun ƴancin kai, amma ƙasashjen duniya ba su yarda da ita ba.

Sir Mo ya ce, yana ɗan shekara takwas zuwa tara aka ɗauke shi daga gida zuwa wajen wani iyali a Djibouti.

Daga can sai wata mata da bai taɓa saninta ba kuma ba shi da alaƙa da ita ta ɗauke shi zuwa Birtaniya.

Ta ce, masa za a kai shi Turai ne, domin ya zauna a wajen wasu dangi – lamarin da ya yi matuƙar faranta masa rai, in ji shi.

“Ban taɓa hawa jirgi ba,” ya ce. Matar ta ce masa ya ce sunansa Mohamed.

Ya ce an ba shi takardun bogi na tafiya da ke ɗauke da hotonsa da sunan “Mohamed Farah” a gefe.

uanguard news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp