Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar sojojin saman Najeriya NAF a karkashin Operation Hadin Kai, sun kai hari kan wasu muhimman maboyar ‘yan Boko Haram a Tumbumma Baba da Chiralia a kudancin Tumbuns na jihar Borno.
Air Commodore Ehimen Ejodame, Daraktan Hulda da Jama’a da Yada Labarai na Hedkwatar Rundunar Sojojin Sama ta Najeriya ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar, inda ya kara da cewa, “aikin sahihan bayanan sirri, jirgin NAF ya kai hari kan wasu gine-ginen ‘yan ta’adda da aka ruwaito ana amfani da su wajen adanawa da hada kai, inda suke kai hare-hare kai tsaye tare da gurgunta hare-haren da aka shirya domin kawo cikas ga bukukuwan Sallah.
Sanarwar ta ce, harin da aka kai ta sama ya halaka ‘yan ta’adda da dama tare da lalata wasu muhimman kayayyakin aiki a yayin farmakin.
“Wannan mataki na riga-kafin,” a cewar Ejodame, “yana jaddada kudurin sojojin saman Najeriya na kare rayukan fararen hula da kuma tallafawa manufofin tsaron kasa.”