Rundunar ‘yan sandan jihar Anambra, ta tabbatar da cewa an kai hari kan ma’aikatan hukumar zabe mai zaman kanta, INEC da wasu ma’aikatan.
Tochukwu Ikenga, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Anambra a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai ya ce ma’aikatan INEC na samun horo lokacin da ‘yan bindigar suka kai hari.
Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Ma’aikatan INEC tare da wasu jami’an hukumar zabe, daliban jami’a da kAnuma wasu jami’an MDA kan shirin horas da ma’aikatan Adhoc a babban zaben 2023 da ke tafe, ‘yan bindiga sun tarwatsa su.
“Babu wani rai da aka rasa, yayin da rundunar hadin guiwar jami’an tsaro suka yi nasarar ceto tare da hana ‘yan bindiga cutar da jami’an zabe a wani aiki a makarantar sakandare ta Ukpor, karamar hukumar Nnewi ta Kudu.
“An tsaurara matakan tsaro na hadin gwiwa a yankin kuma ana ci gaba da kokarin zakulo masu aikata laifuka.”
Ikenga ya tabbatar wa jama’a dabarun aikin ‘yan sanda da Kwamishinan ‘yan sandan Jihar Anambra, Echeng Echeng ya dauka na da karfi da kuzari kuma za su iya magance duk wata matsala ta gaggawa da tsaro, kuma za ta tabbatar da zaben 2023 ba tare da tangarda ba a jihar.