fidelitybank

An kai hari kan ma’aikatan INEC a Anambra

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Anambra, ta tabbatar da cewa an kai hari kan ma’aikatan hukumar zabe mai zaman kanta, INEC da wasu ma’aikatan.

Tochukwu Ikenga, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Anambra a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai ya ce ma’aikatan INEC na samun horo lokacin da ‘yan bindigar suka kai hari.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Ma’aikatan INEC tare da wasu jami’an hukumar zabe, daliban jami’a da kAnuma wasu jami’an MDA kan shirin horas da ma’aikatan Adhoc a babban zaben 2023 da ke tafe, ‘yan bindiga sun tarwatsa su.

“Babu wani rai da aka rasa, yayin da rundunar hadin guiwar jami’an tsaro suka yi nasarar ceto tare da hana ‘yan bindiga cutar da jami’an zabe a wani aiki a makarantar sakandare ta Ukpor, karamar hukumar Nnewi ta Kudu.

“An tsaurara matakan tsaro na hadin gwiwa a yankin kuma ana ci gaba da kokarin zakulo masu aikata laifuka.”

Ikenga ya tabbatar wa jama’a dabarun aikin ‘yan sanda da Kwamishinan ‘yan sandan Jihar Anambra, Echeng Echeng ya dauka na da karfi da kuzari kuma za su iya magance duk wata matsala ta gaggawa da tsaro, kuma za ta tabbatar da zaben 2023 ba tare da tangarda ba a jihar.

nigeria news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp