Rundunar ‘yan sandan jihar Abia, ta tabbatar da kai hari kan ayarin motocin kwamishinan kasuwanci da zuba jari na jihar Abia, Dakta Chimezie Isaac Ukaegbu.
Lamarin ya faru ne a ranar Talata lokacin da kwamishinan ya fara rangadin sanin makamar kasuwanci a cikin babban birnin na Aba.
Maharan a cewar rundunar ‘yan sandan sun bude wuta ne kan ayarin motocin da ke kan hanyarsu ta zuwa kasuwar Ekeoha da ke garin Aba, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar ‘yan sanda biyu.
Wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na ‘yan sanda, PPRO, ASP Maureen Chioma, ya fitar ranar Laraba, ta yi Allah-wadai da wannan aika-aikar na matsorata, inda ta ce rundunar ta ci gaba da dagewa wajen ganin an gurfanar da wadanda suka aikata laifin a gaban kuliya.
“Muna kira ga jama’a da su kwantar da hankalinsu, su lura, tare da ba jami’an tsaro cikakken hadin kai.
“Duk wani bayani, ba tare da la’akari da yadda yake da muhimmanci ba, zai iya zama muhimmi wajen ganowa da kuma kama masu laifin da suka aikata wannan danyen aikin.
Sanarwar ta kara da cewa, “A karshe, muna jaddada kudurinmu na tabbatar da adalci da kuma tabbatar da nasarar da aka samu kan mummuna”.