Wani rahoto da tashar Channels ta ruwaito daga cibiyar Zamfara Circle Community Initiative ya bayyana cewa a mako ɗaya, an kai hari a ƙauyuka 15 a tsakanin 4 zuwa 10 ga watan Agusta.
Rahoton cibiyar ya ce hare-haren sun yi sanadiyar garkuwa da kusan mutum 144, sannan an kashe kusan mutum 24 tare da jikkata wasu mutum 16.
Rahoton ya ƙara da cewa garuruwan da aka kai wa harin su ne: Sabe da Tungar Yamma da Sauru da Lambasu da Dogon Madacci da Dankalgo da Kwanar Kalgo a ƙaramar hukumar Bakura.
A ƙaramar hukumar Tsafe, rahoton ya nuna cewa an kai harin a garuruwan Chediya da Kucheri da Yankuzo da Katangar Gabas Bilbils.
A ƙaramar hukumar Mafara kuma, ƙungiyar ta ce an kai harin a Tabkin Rama da Matsafa da Ruwan Gizo, sai kuma Rafin Jema da ke Gummi da Adabka da Masu a ƙaramar hukumar Bukkuyum.