fidelitybank

An kai hare-hare 60 gabanin zaben 2023 – CDD

Date:

Akalla hare-hare 60 aka kai tare kuma da kashe mutum tara a lokacin yakin neman zaɓe a faɗin Najeriya, gabanin zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar tarayya da za a gudanar a ranar Asabar.

Cibiyar Tabbatar da Dimokuraɗiyya da Ci Gaba CDD, ce ta bayyana hakan a cikin wani rahoto da ta fitar gabanin shiga rumfunan zabe domin kaɗa kuri’a, inda ta ce wasu da dama kuma sun jikkata a hare-haren da aka kai tun fara yakin neman zaɓe a watan Satumban 2022.

CDD ta ce batun rashin tsaro da ƙarancin man fetur da na kuɗi da kuma sauran abubuwa za su iya kawo cikas ga yadda zaɓen zai gudana.

“A karshen shekarar 2022, rikice-rikicen da ke da alaƙa da siyasa sun ƙaru tun bayan zaɓen 2019 da aa gudanar. Alkaluman da muka tattara ya nuna cewa an kai hari sau 60 a lokacin yakin neman zaɓe, inda mutum tara suka mutu,” in ji CDD.

Kungiyar ta kuma nuna damuwa kan yadda ta ce ‘yan siyasa na ɗaukar ‘yan bangar siyasa domin kawo cikas a zaɓen da za a gudanar, inda ta ce hakan zai ƙara janyo taɓarɓarewar matsalar tsaro.

Cibiyar ta yi kira jam’iyyun siyasa da su tabbatar da cewa mambobin da kuma magoya bayansu sun bi sahun sharuɗan da aka kwamitin zaman lafiya ya zartas yayin lokacin saka hannu a yarjejeniyar yin zaɓe lami lafiya.

legit news 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp