fidelitybank

An kafa kwamitin da zai binciki Tambuwal

Date:

Gwamnatin jihar Sokoto, ta kafa wani kwamiti da zai bincike batun mallakar filaye da yadda aka sayar da ko a ka yi gwanjon kadadrorin gwamnati a zamanin mulkin tsohon gwamnan jihar Sanata Aminu waziri Tambuwal.

Cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran gwamnan jihar, Abubakar Bawa ya fitar, ya ce kwamitin mai mutane biyar ƙarƙashin jagorancin Justice M.A. Pindiga, zai kuma duba asusun gwamnatin jihar domin gano adadin kuɗaɗen da aka samu sakamakon sayar da kadarorin.

Sanarwar ta kara da cewa, kwamitin zai kuma duba batun filayen da sabuwar gwamnatin ta ke zargin gwamnatin da ta shuɗen ta rabar ciki har da gidajen gwamnatin jihar da aka yi yi gwanjonsu.

Haka kuma akwai batun motocin gwamnatin jihar da na kananan hukumomi.

Sauran mambobin kwamitin sun haɗar da Barrister Nasiru Muhammed Binji a matsayin sakatare, sai Chief Jacob E. Ochidi, SAN, da Alhaji Usman Abubakar da kuma Barrister Lema Sambo Wali a matsayin mambobi.

An bai wa kwamitin watanni biyu domin gabatar da rahoton sakamkon bicikensa.

nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp