Babban sifeton ‘yan sanda, Usman Baba Alkali, ya kafa kwamiti na musamman domin binciken zarge-zargen kashe-kashe da ake yi wa jami’an rundunar a jihar Anambra.
Rahotonni a kafofin sada zumunta sun zargi wasu jami’an ‘yan sandan a jihar da nuna rashin ƙwarewar aiki, tare da aikata kisan kai.
A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar Olumuyiwa Adejobi ya fitar ranar Juma’a ya ce jami’an da ake zargin sun bayyana a shalkwatar rundunar da ke Abuja kan zarge-zargen da ake yi musu na kisan kai.
Adejobi ya ce jami’an sun hallara a harabar shalkwarat rundunar ne bisa umarnin sifeton ‘yan sandan ƙasar na fara gudanar da bincike, domin gano ainihin gaskiya kan zarge-zargen da ake yi musu tare da ɗaukar matakin da ya dace a kansu.
An dai bai wa kwamitin mako biyu da ya gabatar da sakamakon binciken nasa.