Gwamantin jihar Edo ta kafa kwamitin tantance kadarorin jihar mai mambobi 14 da zai binciki gwamantin da ta gada.
Gwamnatin ta ce kwamitin zai fara aikinsa daga gobe Talata 26 ga wannan watan.
Kafa kwamitin na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren watsa labarai na gwamnan Fred Itua, inda ya ce gwamna Monday Okpebholo ya kafa kwamitin ne ƙarƙashin Dr Ernest Afolabi Umakhihe.
Tuni ɓangaren tsohon gwamnan jihar, Godwin Obaseki suka bayyana binciken da bita-da-ƙulli.