fidelitybank

An kaddamar da gidan adana magunguna a Yobe

Date:

A kuduri aniyar tabbatar da samar da magunguna cikin gaggawa da sauran kayayyakin amfanin al’umma, Hukumar Kula da Magunguna ta Jihar Yobe (YODMA) ta kaddamar da Gidan ajiye magunguna na shiyar Potiskum.

A jawabinsa na bude taron, babban sakataren hukumar, YODMA, Pharmacist Abdulaziz Garba Mohammed ya bayyana cewa, gidan ajiyar zai rika kula da kananan hukumomi hudu na Fune, Fika, Potiskum da Nangere a maimakon tuka mota zuwa Damaturu babban birnin jihar domin kai kayayyakin ya ce, “Wannan wani bangare ne na burinmu na kusantar da ayyuka ga al’ummomi, mun yi imanin ta haka za mu rage farashin sufuri, lokacin da cibiyoyin ke kashewa domin zuwa Damaturu, yanzu za su kai ga majinyatansu cikin gaggawa.”

A nasa bangaren, Manajan shirin ceto rayuka miliyan daya na jihar Yobe (SOML-PforR), Dokta Babagana Abba ya bayyana cewa, ceton rayukan miliyan daya ya kasance babban hadin gwiwa wajen tallafa wa fannin kiwon lafiya “domin abin da muke yi shi ma. A takaice dai mun yi aiki kafada da kafada da gwamnatin jihar Yobe”.

A cewarsa, kafa rumbun ajiyar na shiyyar zai yi saurin mayar da magungunan da suke amfani da su da kuma inganta hanyoyin da abokan huldar su ke amfani da su a fadin shiyyar.

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, Gwamnan Jihar Yobe Mai Mala Buni wanda ya samu wakilcin Kwamishinan Lafiya da Jin Dadin Jama’a, Dr Muhammad Lawan Gana, ya taya hukumar ta YODMA murnar samun ci gaba. “Kamar yadda nake magana yanzu, mun yi tafiya a Gashua, Nguru, Potiskum da Damaturu yayin da muke sa ran sauran biyun”.

legit news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp