A kuduri aniyar tabbatar da samar da magunguna cikin gaggawa da sauran kayayyakin amfanin al’umma, Hukumar Kula da Magunguna ta Jihar Yobe (YODMA) ta kaddamar da Gidan ajiye magunguna na shiyar Potiskum.
A jawabinsa na bude taron, babban sakataren hukumar, YODMA, Pharmacist Abdulaziz Garba Mohammed ya bayyana cewa, gidan ajiyar zai rika kula da kananan hukumomi hudu na Fune, Fika, Potiskum da Nangere a maimakon tuka mota zuwa Damaturu babban birnin jihar domin kai kayayyakin ya ce, “Wannan wani bangare ne na burinmu na kusantar da ayyuka ga al’ummomi, mun yi imanin ta haka za mu rage farashin sufuri, lokacin da cibiyoyin ke kashewa domin zuwa Damaturu, yanzu za su kai ga majinyatansu cikin gaggawa.”
A nasa bangaren, Manajan shirin ceto rayuka miliyan daya na jihar Yobe (SOML-PforR), Dokta Babagana Abba ya bayyana cewa, ceton rayukan miliyan daya ya kasance babban hadin gwiwa wajen tallafa wa fannin kiwon lafiya “domin abin da muke yi shi ma. A takaice dai mun yi aiki kafada da kafada da gwamnatin jihar Yobe”.
A cewarsa, kafa rumbun ajiyar na shiyyar zai yi saurin mayar da magungunan da suke amfani da su da kuma inganta hanyoyin da abokan huldar su ke amfani da su a fadin shiyyar.
Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, Gwamnan Jihar Yobe Mai Mala Buni wanda ya samu wakilcin Kwamishinan Lafiya da Jin Dadin Jama’a, Dr Muhammad Lawan Gana, ya taya hukumar ta YODMA murnar samun ci gaba. “Kamar yadda nake magana yanzu, mun yi tafiya a Gashua, Nguru, Potiskum da Damaturu yayin da muke sa ran sauran biyun”.