fidelitybank

An kaddamar da gidan adana magunguna a Yobe

Date:

A kuduri aniyar tabbatar da samar da magunguna cikin gaggawa da sauran kayayyakin amfanin al’umma, Hukumar Kula da Magunguna ta Jihar Yobe (YODMA) ta kaddamar da Gidan ajiye magunguna na shiyar Potiskum.

A jawabinsa na bude taron, babban sakataren hukumar, YODMA, Pharmacist Abdulaziz Garba Mohammed ya bayyana cewa, gidan ajiyar zai rika kula da kananan hukumomi hudu na Fune, Fika, Potiskum da Nangere a maimakon tuka mota zuwa Damaturu babban birnin jihar domin kai kayayyakin ya ce, “Wannan wani bangare ne na burinmu na kusantar da ayyuka ga al’ummomi, mun yi imanin ta haka za mu rage farashin sufuri, lokacin da cibiyoyin ke kashewa domin zuwa Damaturu, yanzu za su kai ga majinyatansu cikin gaggawa.”

A nasa bangaren, Manajan shirin ceto rayuka miliyan daya na jihar Yobe (SOML-PforR), Dokta Babagana Abba ya bayyana cewa, ceton rayukan miliyan daya ya kasance babban hadin gwiwa wajen tallafa wa fannin kiwon lafiya “domin abin da muke yi shi ma. A takaice dai mun yi aiki kafada da kafada da gwamnatin jihar Yobe”.

A cewarsa, kafa rumbun ajiyar na shiyyar zai yi saurin mayar da magungunan da suke amfani da su da kuma inganta hanyoyin da abokan huldar su ke amfani da su a fadin shiyyar.

Da yake jawabi yayin kaddamar da aikin, Gwamnan Jihar Yobe Mai Mala Buni wanda ya samu wakilcin Kwamishinan Lafiya da Jin Dadin Jama’a, Dr Muhammad Lawan Gana, ya taya hukumar ta YODMA murnar samun ci gaba. “Kamar yadda nake magana yanzu, mun yi tafiya a Gashua, Nguru, Potiskum da Damaturu yayin da muke sa ran sauran biyun”.

spw

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp