Rundunar tsaron sojin saman Najeriya, ta ce za ta yi bincike kan zargin cewa jirgin yaƙin soji ya kashe mutum shida bisa ‘kuskure’ a lokacin da sojojin ke bin wani gungun ƴan bindiga a jihar Katsina.
A cikin wata sanarwa da daraktan sashen yaɗa labarai da hulɗa da jama’a na shelkwatar rundunar, Air Vice Marshal Olusola F Akinboyewa ya fitar, ya ce Rundunar ta yi matuƙar damuwa da rahotannin, kuma babban hafsan sojojin saman Najeriya, Air Marshal Hassan Abubakar ya bayar da umurnin gudanar da cikkaken bincike da kuma ɗaukar matakan da suka dace.
A ƙarshen mako ne rahotanni daga jihar Katsina, mai fama da matsalar ƴan bindiga a arewa maso yammacin Najeriya, suka bayyana cewa wani jirgin sojin saman Najeriya ya kai hari kan fararen hula, lamarin da ya haifar da asarar rayuka.
Sojojin Najeriya sun yi ƙaurin suna wajen kai harin kuskure kan fararen hula a ƴakin da suke yi da matsalar tsaro a yankunan Najeriya.
Sai dai a cikin sanarwar da ta fitar a yau Litinin, rundunar ta ce sojojin sama da ke aiki ƙarakshin dakarun Fansar Yamma sun yi nasara a harin da suka kai a tsaunin Yauni a gundumar Zakka da ke karamar hukumar Safana a jihar Katsina inda suka yi nasarar kashe ƴan bindiga da dama kuma suka taimaka wajen daƙile harin da aka kai wa ƴansanda da kuma ƴan sinitirin jihar Katsina.
Ya kuma ce sun kai harin ne bayan samun sahihan bayanai da ke nuna cewa an kai wa yankin da ƴansandan suke hari inda aka kashe jami’ai biyu da ƴan sintiri huɗu, kuma an samu tabbacin cewa ƴan bindigar na boye a tsaunin Yauni da ke kusa da yankin kafin kai harin.