fidelitybank

An kaddamar da bincike kan lugudan wuta a Katsina da sojoji su ka yi

Date:

Rundunar tsaron sojin saman Najeriya, ta ce za ta yi bincike kan zargin cewa jirgin yaƙin soji ya kashe mutum shida bisa ‘kuskure’ a lokacin da sojojin ke bin wani gungun ƴan bindiga a jihar Katsina.

A cikin wata sanarwa da daraktan sashen yaɗa labarai da hulɗa da jama’a na shelkwatar rundunar, Air Vice Marshal Olusola F Akinboyewa ya fitar, ya ce Rundunar ta yi matuƙar damuwa da rahotannin, kuma babban hafsan sojojin saman Najeriya, Air Marshal Hassan Abubakar ya bayar da umurnin gudanar da cikkaken bincike da kuma ɗaukar matakan da suka dace.

A ƙarshen mako ne rahotanni daga jihar Katsina, mai fama da matsalar ƴan bindiga a arewa maso yammacin Najeriya, suka bayyana cewa wani jirgin sojin saman Najeriya ya kai hari kan fararen hula, lamarin da ya haifar da asarar rayuka.

Sojojin Najeriya sun yi ƙaurin suna wajen kai harin kuskure kan fararen hula a ƴakin da suke yi da matsalar tsaro a yankunan Najeriya.

Sai dai a cikin sanarwar da ta fitar a yau Litinin, rundunar ta ce sojojin sama da ke aiki ƙarakshin dakarun Fansar Yamma sun yi nasara a harin da suka kai a tsaunin Yauni a gundumar Zakka da ke karamar hukumar Safana a jihar Katsina inda suka yi nasarar kashe ƴan bindiga da dama kuma suka taimaka wajen daƙile harin da aka kai wa ƴansanda da kuma ƴan sinitirin jihar Katsina.

Ya kuma ce sun kai harin ne bayan samun sahihan bayanai da ke nuna cewa an kai wa yankin da ƴansandan suke hari inda aka kashe jami’ai biyu da ƴan sintiri huɗu, kuma an samu tabbacin cewa ƴan bindigar na boye a tsaunin Yauni da ke kusa da yankin kafin kai harin.

leadership news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp