Majalisar zartaswar jihar Kaduna ta janye dokar hana fita da aka sanya a fadin jihar dama Zaria bayan kyakkyawan nazari tare da tabbatar da komai ya dai-daita a jihar.
Majalisar karkashin jagorancin gwamna Uba Sani, ta ce an janye dokar hana fitar da ke aiki a yanzu daga karfe 8 na safe zuwa 6 na yamma gaba É—aya.
Dokar za ta fara aiki ne daga yau Talata.
To sai dai kuma Majalisar zartaswar ta buÆ™aci al’ummar jihar da su kiyaye doka da kuma kaucewa shiga duk wani rikici ko tashin hankali da zai iya kawo wa jihar matsala.
An kuma buÆ™aci mazauna jihar da su kaucewa gudanar da duk wani taro ba bisa Æ™a’ida ba.
Daga nan gwamnatin jihar ya sha alwashin tabbatar da tsaron rayuka da ma dukiyoyi al’umma.
An sanya dokar hana fitar ce bayan tarzomar da ta ɓarke a lokacin zanga-zangar matsin rayuwar da aka yi a fadin Najeriya.