fidelitybank

An harbi magoyin bayan Arsenal yayin murnar cin Man Utd

Date:

Ana zargin cewa wani jami’in tsaro ya harbe wani magoyin bayan Arsenal a Uganda, lokacin da yake murnar nasarar da ƙungiyarsa ta samu kan Manchester United a gasar Firimiyar Ingila ranar Laraba.

An kuma jikkata wani yayin da jami’in tsaron ya buɗe wuta kan dandazon muagoya bayan Arsenal da ke murna a wani wajen cin abinci a garin Lukaya, mai nisan kilomita 100 da Kampala babban birnin ƙasar.

Lamarin ya faru ne ana daf da kammala buga wasan, wanda Arsenal ta samu nasara da 2-0.

Wani ɗan jarida a yankin ya faɗa wa BBC cewa mai kula da wajen da ake kallon wasan ya fusata da irin hayaniyar da magoyan Arsenal ɗin ke yi, inda ya buƙaci jami’in tsaron da ya ɗauki mataki.

Sai dai mutanen ba su saduda ba, inda suka ci gaba da murna da sowa.

Wani shaida ya faɗa wa ɗan jaridar cewa, mai wajen cin abincin da kuma ake kallon wasan ya kashe injin da ke bayar da hasken wuta a wajen, abin da ya fusata masu kallon har ta kai suka ƙara ihu fiye da farko.

A lokacin ne kuma ake zargin mai gadin wurin ya buɗe musu wuta.

An ruwaito cewa wanda lamarin ya rutsa da shi John Ssenyonga, mai shekara 30, ya mutu nan take a wajen.

An kuma garzaya da wani magoyin bayan Arsenal ɗin Lawrence Mugejera zuwa asibiti bayan samun raunuka.

Mai gadin da kuma manajan da ke kula da wurin sun tsere bayan faruwar lamarin, inda jamin’an tsaron ke ci gaba da farautarsu.

vgn news 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp